| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
'Yan sandan Ghana sun kama gomman masu zanga-zanga
Kungiyar ta shirya zanga-zanga ne don matsa wa gwamnatin kasar Ghana lamba kan yadda take tafiyar da tattalin arzikin kasar da kuma halin matsin rayuwa da al'ummar kasar ke ciki.
'Yan sandan Ghana sun kama gomman masu zanga-zanga
'Yan sandan Ghana sun ce mutanen sun keta dokar hana  zanga-zanga./Hoto: Rundunar 'yan sandan Ghana / Others
22 Satumba 2023

Rundunar 'yan sandan Ghana ta kama masu zanga-zanga 49 a gaban fadar shugaban kasar (Jubilee House) da ke birnin Accra a ranar Alhamis, kamar yadda ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

'Yan sandan sun ce sun kama masu zanga-zangar ne saboda yadda wadanda suka shirya ta wato kungiyar Democracy Hub ta yi "biris da hukuncin kotu wanda ya hana ta yin zanga-zanga a kusa da kuma kewayen fadar shugaban kasa daga ranar 21 zuwa 23 ga watan Satumban 2023," a cewar sanarwar.

Kungiyar ta shirya zanga-zanga ne don matsa wa gwamnatin kasar Ghana lamba kan yadda take tafiyar da tattalin arzikin kasar da kuma halin matsin rayuwa da al'ummar kasar ke ciki.

Masu zanga-zangar sun ce wasu mutane da suka zo kallon zanga-zangar sanye da bakaken da jajayen kaya – launuka da ake alakantawa da masu zanga-zangar kin jinin gwamnati da tsadar rayuwa – su ma an kama su.

A nata bangaren rundunar 'yan sandan kasar, ta ce ba ta hana mutane 'yancinsu na yin zanga-zangar ba, idan har suna da tarihin yin zanga-zangar lumana a baya.

Rundunar ta ce abin da ya sa ba za ta amince da yin zanga-zangar a gaban fadar shugaban kasa ba shi ne "saboda waje ne mai cikakken tsaro da muhimmanci," a cewar sanarwar.

Gwamnatin Shugaba Nana Akufo-Addo tana ikirarin cewa matsalar tattalin arzikin da kasar take ciki tasirin annobar korana da yakin Rasha da Ukraine ne, wanda kuma ya haifar da tashin farashin kayayyaki a kasashen duniya da dama.

MAJIYA:TRT Afrika