| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Turkiyya ta yi tir da Israila kan amincewa da Somaliland
Turkiyya ta yi kakkausar suka kan matakin Isra'ila na amince wa da Somaliland a matsayin kasa mai 'yancin kai.
Turkiyya ta yi tir da Israila kan amincewa da Somaliland
Turkish Head of Communications Burhanettin Duran says Israel's recognition of Somaliland is a violation of Somalia's sovereignty. / AA
27 Disamba 2025

Turkiyya ta yi kakkausar suka kan matakin Isra'ila na amince wa da Somaliland a matsayin kasa mai 'yancin kai.

A ranar Juma'a, Hukumar Sadarwa ta Turkiyya ta bayyana matakin na Tel Aviv a matsayin "keta doka ta ƙasa da ƙasa ƙarar" da kuma "tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Somaliya."

"Wannan mataki yana nufin kai hari ga 'yancin kai da cikakken ikon ƙasa na Somaliya, kuma zai ara ƙara taɓarɓara yanayin da ke ciki yankin (Kusurwar Afirka) wanda yake da rauni," in ji Burhanettin Duran, Shugaban Sadarwa na Turkiyya.

"Wannan matsayi na daga cikin ayyukan rashin tunani na gwamnatin (Firaministan Isra'ila Benjamin) Netanyahu, wadda ke da baƙin tarihin na kisan aƙre dangi da mamaya, kuma wadda ke daƙile yunuƙrin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin," in ji Duran a cikin wata sanarwar da aka fitar a hukumance.

Allah wadai a matakin duniya

Yayin da yake sake jaddada goyon bayan Turkiyya ga 'yancin Somaliya, Shugaban Sadarwar na Turkiyya ya ce: "Ina ga ya kamata al'ummar duniya ta ɗauki matsaya ɗaya kan irin waɗannan matakai waɗanda za su ƙara dagula al'amura da kuma ƙara dagular matsalar tsaro a Kusurwar Afirka."

A ranar Juma'a, matakin Isra'ila ya jawo suka daga duniya baki daya, ciki har da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), da Ƙungiyar Haɗin Kan Larabawa, da Hukumar Falasdinu, saboda ta amince da Somaliland, wani yanki a arewacin Somaliya wanda yake cikin iyakokin Jamhuriyar Tarayyar Somaliya.

A nata ɓangaren, Somaliya ta yi tir da wannan mataki na tsokana na Isra'ila, inda ta bayyana matakin Tel Aviv a matsayin keta 'yancinta da cikakken ikon yankinta.

Rumbun Labarai
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela