| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Da tsakar daren Alhamis ɗin nan ne a wani saƙo ta shafin sada zumunta na Truth Social, Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa Ma'aikatar Yaƙi ta ƙasarsa ta kai hare-hare a kan 'yan ta'adda na ƙungiyar ISIS (Daesh) a arewa maso yammacin Nijeriya.
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Tun a baya dai Trump ya saka Nijeriya a jerin kasashe masu damuwa ta musamman bisa zargin ana aikata kisan kare dangi ga Kiristocin kasar. / Reuters

Ma’aikatar Harkokin Wajen Nijeriya ta tabbatar da hare-haren da Amurka ta kai a Jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin ƙasar, tana mai cewa da haɗin gwiwar ƙasar aka kai su.

Wata sanarwa daga ma’aikatar Harkokin Wajen Nijeriya da ta biyo bayan sanarwar shugaban Amurka Donald Trump da Cibiyar Bayar da Umarni ta Sojin Amurka a Afirka (AFRICOM) ta nuna cewa hukumomin Nijeriya suna da masaniya kan harin da Amurka ta kai a yankin Sokoto na arewa maso yammacin Nijeriya.

Hasali ma, sanarwar wadda Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Nijeriya KImiebi Imomotimi Ebienfa ya fitar ta bayyana cewa da amincewa da haɗin gwiwarta hakan ta tabbata.

A cewar sanarwar, an kai harin ne domin kawar da barazanar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi, tana mai cewa hare-haren ba su da alaƙa da addini tun da dai ‘yan ta’adda suna kashe kowa, ciki har da Musulmai da Kirista.

“Bisa yin la’akari ga ayyukan ƙasa da ƙasa da kuma yarjeniyoyin fahimtar juna na aiki tare, wannan haɗin gwiwa ya haɗa da musayar bayanan sirri, dabarun gudanar da ayyuka, da sauran taimakon juna da suka yi daidai da dokokin ƙasa da ƙasa na girmama ikon juna da tabbatar da aniyar bai-ɗaya ta samar da tsaro a duniya,” sanarwar ta bayyana.

Masu AlakaTRT Afrika - Jiragen Amurka na nazarta da tattara bayanan sirri kan Nijeriya bayan barazanar Trump: Reuters

Sanarwar ta kuma ce duk wani matakin da za a ɗauka na yaki da ta’addanci yana da manufar kare rayukan fararen-hula, kare haɗin kan ƙasa, da kare ‘yanci da mutuncin dukkan ‘yan ƙasa ba tare da la’akari da ƙabila ko addini ba.

Kazalika sanarwar ta ce “Aikata kowane irin ta’addanci a kan Kiristoci, Musulmai ko wasu wasu al’ummu na daban ya saɓa wa aƙidun Nijeriya da tsaro da zaman lafiyar ƙasa da ƙasa.”

An kuma bayyana cewa gwamnatin tarayyar Nijeriya za ta ci gaba da mu’amala da ƙawance ta tabbatattun hanyoyin diflomasiyya da tsaro don kassara ‘yan ta’adda, katse hanyoyin samun kuɗaɗe da kayan aikinsu, dakatar da barazanar tsallaka iyaka da kuma inganta ƙarfin tsaro da tattara bayanan sirri na Nijeriya.

A ƙarshe sanarwar ta ce Nijeriya za ta ci gaba da aiki da kawayenta kuma ma’aikatar Harkokin Waje za ta dinga sanar da jama’a ko me ake ciki ta hanyoyin da suka kamata.

Masu AlakaTRT Afrika - Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump

Da tsakar daren Alhamis ɗin nan ne a wani saƙo ta shafin sada zumunta na Truth Social, Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya sanar cewa Ma'aikatar Yaƙi ta ƙasarsa ta kai hare-haren a kan 'yan ta'adda na ƙungiyar ISIS (Daesh) da ke arewa maso yammacin Nijeriya.

Kuma jim kaɗan bayan sanarwar ta Trump, Cibiyar Bayar da Umarni ta Sojin Amurka a Afirka (AFRICOM) ta tabbatar da kai harin.

Sanarwar da AFRICOM suka fitar ta shafin X ta ce an kai harin ne a yankin jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Nijeriya.

Rumbun Labarai
Yunwa ta kai mummunan mataki da bai taɓa kai wa ba a shekaru 10 a Arewacin Nijeriya - WFP
Sojojin Nijeriya sun kashe ’yanta’adda 662, sun ceto 951 da aka sace cikin watanni uku
CBN ya soke lasisin ƙananan bankuna na Microfinance 46 saboda rashin cika ƙa’idoji
Nijeriya ta yi alƙawarin tallafa wa 'yan ƙasar 271 da suka dawo daga Afirka ta Kudu
Ɗan Nijeriya ya mutu bayan sakinsa daga kurkuku a Côte d'Ivoire
Gwamnatin Nijeriya ta karɓi 'yan ƙasar 269 da aka sake mayarwa gida daga Afirka ta Kudu
Jam'iyyar adawa ta NDC a Nijeriya ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin kotu game da rajistarta
Sojojin Nijeriya sun ceto ɗalibai da malaman GDSS Lassa 10 a Jihar Borno
Dakarun Nijeriya sun ce manyan kwamandojin DAESH sun miƙa wuya sakamakon ƙara matsin lambar soji
An kama mutane 10 da ake zargi da kashe shugaban ƙungiyar Fulani ta MACBAN na jihar Benue a Nijeriya
Sojoji sun kashe Lakurawa biyu da ƙwato makamai a Arewa Maso Yammacin Nijeriya
DSS ta saki mutumin da aka tsare saboda zargin alaƙa da Boko Haram bisa kuskure, ta biya shi diyya
'Yanbindiga a Nijeriya sun kashe manoma 17 a Jihar Zamfara
An gurfanar da ƙarin mutum 17 bayan tuhumar 33 bisa zargin kisan Malamar Islamiyya a Kaduna
Sojojin Nijeriya sun ceto fararen-hula 53 tare da ƙwato motoci takwas a Borno
Mutum aƙalla takwas sun mutu, an ceto 26 bayan bene mai hawa uku ya rushe a Legas
Kotu a Nijeriya ta yanke wa mutum uku hukuncin kisa ta rataya, ciki har da wani ɗan ƙasar waje
'Yansanda a Nijeriya sun kama 'yan kasashen waje 38, sun ƙwato makamai a jihar Legas
CBN ya ƙaddamar da jakadun kare martabar naira a ƙasar
Mutum 20 sun mutu a wani hari da aka kai a Jihar Filato a Nijeriya - 'Yansanda