TURKIYYA
3 MINTI KARATU
An yi gangamin nuna goyon bayan Falasɗinawa a Istanbul a farkon shekerar 2025
Dubban mutane da suka idar da sallar Asuba ne suka yi gangami zuwa Gadar Galata, tare da ƙungiyoyin farar-hula 400, suna masu kira ga Isra’ila ta daina kisan kiyashin da take yi a yankin Falasɗinu.
An yi gangamin nuna goyon bayan Falasɗinawa a Istanbul a farkon shekerar 2025
Dubban mutane ne suka yi gangamin goyon bayan Falasɗinu a Istanbul ranar farko ta shekarar 2025 yayin da yaƙin ƙare-dangin da Isra’ila ta ke yi a Gaza ke ci gaba:Hoto/ AA
1 Janairu 2025

Ɗaruruwan dubban mutane ne suka yi gangami a birnin Istanbul, inda suka halarci wani babban taron da gidauniyar matasan Turkiyya (TUGVA) ta shirya da maudu’in “Farkar da Duniya."

A cikin sa’o’in farko na sabuwar shekara ne dai, mutane da taken ‘Gadar Galata za mu je' suka fara taruwa bayan sun yi sallar Asuba a babban masallaci Aya Sofya domin nuna goyon bayansu ga Falasɗinawa.

Da yawa daga cikin masu gangamin sun saka mayafin keffiyeh domin nuna goyon bayansu ga Gaza kuma sun riƙe kwalaye da rubuce-rubuce kamar "Birnin Ƙudus namu ne," da "Gaza: Inda Yara Ba Sa Girma," da kuma "Birnin Ƙudus na ƙarƙashin Mamaya."

Wasu kuma sun kunna fitilu yayin da suke gangamin, inda suke rera take kamar "Isra’ila mai kisan-kai za ta gurfana a gaban ƙuliya," da "Shahidai ba sa mutuwa," da kuma "Daga Istanbul zuwa Al-Aqsa, dubban gaisuwa ga ‘yan gwagwarmaya."

Bayan sun isa Gadar Galata, masu gangamin sun bi ta shingen ‘yan sanda kafin su shiga wurin taron.

Ƙungiyoyi ba da agaji sun bai wa mahalarta taron shayi da gurasar simit da miya, yayin da hukumomi suka tabbatar da ingantaccen tsaro kusa da masallatan da gadar don tabbatar da da cewa koma ya tafi yadda ya kamata.

Wannan taron ya jaddada alaƙa ta tarihi da al’ada da ke tsakanin Turkiyya da Birnin Ƙudus da ma Masallacin Ƙudus inda mahalarta taron ke kira ga duniya ta ƙara sanin abin da ake ciki tare da ɗaukar mataki don agaza wa Falasɗinawa.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro
Turkiyya ta yi maraba da amincewar majalisar dokokin TRCN kan ƙudurin samar da ƙasashe biyu
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan
Jami'an Turkiyya da Syria sun gudanar da tattaunawa kan tsaro a Ankara