| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Gwamnatin ta yi jaje ga duk wanda ya rasa rayuwarsa sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda, tare da yaba wa dakarun sojojin Nijeriya saboda jajircewarsu wajen kare ƙasar daga makiya.
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Shugaba Tinubu na Nijeriya / Reuters
1 Nuwamba 2025

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra’ayi wanda ta ce wasu masu son rai ne ke da hannun wurin rura wannan wutar.

Wannan na zuwa ne bayan Amurka ta ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ta fitar a ranar Asabar, gwamnati ta ce tana da cikakken kudiri wajen yakar tsattsauran ra’ayi da ‘yan ta’adda, wanda ta bayyana cewa wasu kungiyoyi masu son zuciya ne ke haifar da shi don raba kawunan al’umma da tayar da hankula a yankin Yammacin Afirka da Sahel.

“Mun kuduri aniyar yakar tsattsauran ra’ayi wanda wasu ke amfani da shi wajen kawo rarrabuwar kawuna da lalacewar al’umma,” in ji sanarwar.

Gwamnatin ta yi jaje ga duk wanda ya rasa rayuwarsa sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda, tare da yaba wa dakarun sojojin Nijeriya saboda jajircewarsu wajen kare ƙasar daga makiya.

“Muna juyayin wadanda suka mutu sakamakon tsattsauran ra’ayi, tare da girmama dakarunmu masu kwazo wajen yaki da makiya marasa imani,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma jaddada cewa bambancin addini, kabila da al’ada shi ne karfin Nijeriya.

Ma’aikatar ta kuma jaddada kyakkyawar dangantaka tsakanin Najeriya da Amurka, tana fatan hadin gwiwar kasashen biyu zai ci gaba da karfafa zaman lafiya da dimokiradiyya a duniya.

Rumbun Labarai
Jihar Kwara ta sa dokar hana fita ta awa 24 a yankin Oro-Ago saboda matsalar tsaro
"Ina ma a ce abubuwan da suka faru a siyasar Kano mafarki ne": Kwankwaso
Mahaifin kyaftin din Super Eagles Wilfred Ndidi ya mutu sakamakon hatsarin mota
Tinubu ya nemi a ƙara yawan alƙalan Kotunan Ɗaukaka Ƙara da na Tarayya a Nijeriya
Za a gurfanar da wasu sojojin Nijeriya a gaban kotun soji kan yunƙurin kifar da gwamnati
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya shiga Jam'iyyar APC
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya ta ceto mutum 22 daga hannun masu safarar mutane a  Katsina
NDLEA ta kama ’yar Brazil da hodar iblis mafi yawa da aka taɓa kamawa a Nijeriya
’Yansandan Nijeriya sun kama wata mota da ‘abubuwan fashewa’ a Jihar Oyo
Shugaba Tinubu zai kai ziyarar aiki Turkiyya ranar Litinin
‘Yansandan Nijeriya sun kama wata amarya a Jigawa kan zargin kashe angonta da maganin ɓera
Rundunar Sojin Nijeriya ta ƙaryata wani rahoto na zargin mutuwar kurtu a Depot na Zaria
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPP
Turkiyya ta gano kayan tarihi 76 da aka yi amannar na Nijeriya ne da za a mayar da su gida
Yadda ɗaukar ciki da haihuwa ke zama babbar barazana ga miliyoyin mata marasa galihu
‘Yan Nijeriya kusan miliyan 35 na cikin barazanar yunwa, in ji MDD
Dorinar ruwa sun lalata gonaki da dama a Jihar Gombe, manoma sun tafka babbar asara
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yanta'addan Lakurawa, sun kuɓutar da mutane 62 a Kebbi da Zamfara
Matakan da Gwamna Abba ya ɗauka kan kisan gillar mata da ‘ya’yanta shida a Jihar Kano
Dakarun Nijeriya sun gano kabarin bai-daya na 'yan ta'adda a Borno