| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Da yake tabbatar da lamarin kyaftin ɗin Super Eagles, Willam Troost-Ekong, ya ce da zarar an warware matsalar, su da kansu za su sanar da hakan.
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Keftin ɗin Super Eagles, William Troost-Ekong ya tabbatar da lamarin a shafinsa na X
12 Nuwamba 2025

‘Yan wasan tawagar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya, Super Eagles, sun ƙaurace wa atisayen shirin wasannin shiga gasar cin kofin duniya kan rashin biyansu alawus.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, wani ɗan jarida da yake aiki kan harkar wasanni a Nijeriya, Oluwashina Okeleji, ya ce ‘yan wasa da jami’an tawagar ta Super Eagles sun ƙaurace wa atisayen ne saboda batutuwa na alawus alawus da ba biya su ba.  

“[Suna] jiran warware matsalar da wuri domin su ci gaba da shirya wa wasan ranar Alhamis,” in ji Okeleji.

Da yake tabbatar da lamarin kyaftin ɗin Super Eagles, Willam Troost-Ekong, ya ce da zarar an warware matsalar, su da kansu za su fara bayyana hakan.

“Duk wata sanarwa ko iƙirari  ko kuma wata buƙata bayan buƙata [ta alawus] ta gaskiya da aka yi rubutu a kai ba gaskiya ba ce,” in Troost-Ekong, yana mai ishara ga saƙon da Okeleji ya wallafa.

“Abin da muke so kuma muke ci gaba da yi shi ne mu mayar da hankali kan muhimman wasannin da ke gabanmu,” in ji shi.

Nijeriya dai za ta kara da Gabon a wasan neman shiga gasar cin kofin duniya.

Gurbi ɗaya tilo ne ya yi saura da wata ƙasar Afirka za ta iya cikewa a gasar cin kofin duniya ta shekarar 2026 kuma ƙasashen Nijeriya da Gabon da Kamaru da kuma Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ne ke neman samun damar.

Nijeriya za ta kara da Gabon ranar Alhamis da misalin ƙarfe biyar agogon Nijeriya yayin da Kamaru za ta kara da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo da misalin ƙarfe takwas agogon Nijeriya.

Ƙasashen da suka yi nasara a wasannin kuma za su kara a ƙarshen mako inda za a samu ƙasar da za ta wakilci Afirka a zagaye na ƙarshe na neman shiga gasar cin kofin duniya.

Za a yi wasannin ranar Alhamis da ƙarshen makon ne a ƙasar Maroko, kuma tuni yawancin ‘yan wasan da kocin Nijeriya ya gayyata suka isa ƙasar da ke arewacin Afirka.

 

Rumbun Labarai
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka