| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
ECOWAS ta yi Allah wadai da yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin
ECOWAS ta ce za ta ci gaba da mara wa Benin baya ta dukkan hanyoyin da suka dace ciki har da yiwuwar tura sojojinta na ko-ta-kwana na yanki don kare ikon kasar da tsarin mulkin ta.
ECOWAS ta yi Allah wadai da yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin
ECOWAS ta kuma yaba wa Gwamnatin Benin da Rundunar Sojin Benin bisa gaggawar da suka yi wajen shawo kan lamarin da dawo da doka da oda. / ECOWAS/X
7 Disamba 2025

 Ƙungiyar ECOWAS ta bayyana matuƙar damuwa bayan samun rahotannin yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, ƙungiyar ta soki abin da ta kira “yunkurin da ya saɓa wa tsarin mulki” wanda ke nufin take wa jama’ar Benin muradunsu.

A cewar ECOWAS, duk wani yunƙurin karɓe mulki ta hanyar ƙarfi barazana ce kai tsaye ga mulkin dimokuraɗiyya da zaman lafiya a yankin.

Ecowas ɗin ta bukaci a mutunta tsarin mulkin Benin gaba ɗaya, tana mai jaddada cewa dole a kare tsare-tsaren dimokuraɗiyya a kowane hali.

ECOWAS ta kuma yaba wa Gwamnatin Benin da Rundunar Sojin Benin bisa gaggawar da suka yi wajen shawo kan lamarin da dawo da doka da oda.

Ta gargadi shugabannin da suka shirya wannan juyin mulkin kan cewa alhakin duk wata asarara rai ko dukiya zai rataya ne a wuyansu.

Yayin da ta sake nanata kudurinta na kare tsarin mulki a yankin, ECOWAS ta ce za ta ci gaba da mara wa Benin baya ta dukkan hanyoyin da suka dace ciki har da yiwuwar tura sojojinta na ko-ta-kwana na yanki don kare ikon kasar da tsarin mulkin ta.

ECOWAS ɗin ta kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankula tare da haɗa kai wajen ganin an tabbatar da kwanciyar hankali gaba ɗaya a Benin.

Rumbun Labarai
‘Yanta’adda sun kashe mutane 14 a arewa maso yammacin Kamaru, in ji gwamnati
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF a Kudancin Kordofan
Uganda ta ba da umarnin katse intanet a yayin da ake gudanar da zaɓen shugaban ƙasa
Trachoma: Ta'azzarar amosanin ido da ke makanta mutane na ƙarfafa fafutukar dawo da gani a Afirka
Wasu wayoyin hannu da aka yi odarsu a shekarar 2010 sun isa Libya bayan shekaru 16
Mitumba: Sake tunani game da kasuwancin tufafin gwanjo a Afirka
Ɗaruruwan mutane sun tsere daga gidajensu a Kudancin Kordofan na Sudan sakamakon sabbin hare-hare
Gwamnatin Sudan ta koma Khartoum bayan fiye da shekaru biyu ana yaƙi
Nijar ta soke ayyukan ɗaruruwan ƙungiyoyi masu zaman kansu na cikin gida da na ƙasashen waje
Guinea-Bissau ta haramta taron manema labarai 'ba tare da izini ba' domin guje wa tashin hankali
Yaƙin Sudan: Sojojin Sudan sun ce sun yi wa sojojin RSF asara a Darfur da Kordofan
Burkina Faso, Mali da Nijar sun yi tir da ɗauke Maduro da Amurka ta yi
Somalia ta musanta satar abincin agaji bayan Trump ya sanar da dakatar da taimako
Yaƙi a Sahel: Ƙalubalen da ke tattare da yaƙar ƙungiyoyin ta'addanci
An kama tsohon Ministan Kudi na Ghana Ken Ofori-Atta a Amurka
An daƙile yunƙurin kifar da gwamnatin Traore na Burkina Faso Traore: minista
Shugaban ƙasar Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Touadera ya samu nasarar yin wa’adi na uku
Kotun Kolin Guinea ta tabbatar da Doumbouya a matsayin wanda ya lashe zaben kasar
Benin da Nijar sun kori jakadun juna a matakin ramuwar gayya
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari