| hausa
AFIRKA
1 minti karatu
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi alhinin rasuwar Dr. Adam Ibrahim Ismail, wanda aka kashe a Al Fasher; tana mai kira da a dinga bai wa ma'aikatan lafiya kariya.
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Tedros ya ce "zaman lafiya shi ne maganin da ya fi kowanne karfi."
10 Nuwamba 2025

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta yi kira da a kawo karshen yakin Sudan bayan da aka kashe wani likita a yankin Al Fasher da rikicin ya fi kamari.

Tedros Adhanom Ghebreyesus ya rubuta a shafin X a ranar Lahadi cewa |Dole a kawo karshen zubar da jini a Sudan.”

Ya ce ya yi “bakin ciki matuka da samun labarin kisan Dr Adam Ibrahim a wani rikicin a yankin Al Fasher na Sudan,” yana mai cewa “WHO ta yi alhinin mutuwar Dr Ismail tare da neman kawo karshen kisan da ake yi wa jami’an lafiya.

Tedros ya kammala sakon nasa da rokon samar da zaman lafiya, yana mai cewa: “Zaman lafiya shi ne maganin da ya fi kowanne karfi.”

A ranar 26 ga watan Oktoba ne mayakan ‘yan-aware na RSF suka kwace iko da Al Fasher suke kuma aikata kisan kiyashi, kamar yadda hukumomin kasa da na duniya ke fada, inda ake gargadin cewa cin zalin da ake yi zai iya shiga wasu yankunan da dama.

Tun watan Afrilun 2023, rundunar sojin Sudan da mayakn RSF suke fafata yakin da ya yi ajalin dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallansu.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD