| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta gargaɗi Amurka: 'Za mu ɗauki kowane irin hari a matsayin cikakken yaƙi a kanmu'
Iran ta ce ba za ta bambance tsakanin ƙaramin hari ko babban hari ba inda ta ce idan Amurka ta kai mata hari za ta mayar mata da martani mai ƙarfi.
Iran ta gargaɗi Amurka: 'Za mu ɗauki kowane irin hari a matsayin cikakken yaƙi a kanmu'
Tehran ta ce ta shirya wa kowane irin yanayi idan Amurka ta kai mata hari / AP
24 Janairu 2026

Iran ta ce za ta ɗauki kowane irin hari a matsayin "cikakken yaƙi a kanmu," in ji wani jami'in Iran mai mukami, yayin da kayan aikin soji na Amurka ke shirin isa Gabas ta Tsakiya cikin 'yan kwanaki masu zuwa.

Jami'in, wanda ya yi magana a bisa sharaɗin rashin bayyana suna a ranar Juma'a, ya ce an sanya sojojin Iran a cikin shirin ko-ta-kwana a yayin da ake dakon isowar jirgin ruwan da ke dakon jiragen saman yaƙin Amurka da kuma sauran dakaru.

"Wannan tarin sojin — muna fatan ba da nufin fito-na-fito bane — amma sojojimu sun shirya kan duk wani abu mafi muni," in ji jami'in.

"Shi ya sa komai ke cikin shirin ko-ta-kwana a Iran."

Jami'in ya yi gargaɗin cewa Tehran ba za ta bambance girma ko ƙanƙantar duk wani hari ba.

Ya ce Iran za ta mayar da martani cikin ƙarfi idan aka kai mata hari.

"Kuma za mu mayar da martani a mafi ƙarfi yadda zai yiwu don warware wannan," in ji jami'in.

'Za mu mayar da martani'

Shugaban Amurka Donald Trump a ranar Alhamis ya bayyana cewa Amurka na da jirgin ruwan dakon jiragen sama da ke hanyar zuwa Iran, amma Trump ɗin ya ce yana fata ba za a yi amfani da jirgin ba.

Jiragen ruwan yaƙin na Amurka ciki har da na dakon jiragen sama na USS Abraham Lincoln, da wasu jiragen saman yaƙi sun fara tafiya a cikin tekun Asia-Pacific a makon da ya gabata.

"Idan Amurkawa suka keta 'yancin Iran da cikakken ikon yankinta, za mu mayar da martani," in ji jami'in. Ya ƙi bayyana takamaiman yadda martanin Iran zai kasance.

"Kasar da ke fuskantar barazanar soja daga Amurka koyaushe ba ta da zaɓi sai ta tabbatar cewa duk abin da take da shi za a iya amfani da shi don mayar da martani, idan zai yiwu, dawo da daidaito kan duk wanda ya yi ƙoƙarin kai hari kan Iran," in ji jami'in.

Rumbun Labarai
Yaƙin da ake yi da ta'addancin Daesh yana ƙara ƙarfi: Erdogan
Turkiyya ba ta goyon bayan tsoma bakin ƙasashe waje a kan Iran – Erdogan
Adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar Iran ya kai  4,000: Rahoto
Syria ta cim ma tsagaita wuta don karɓe iko da arewa maso gabas daga hannun ‘yan ta’addan YPG
Iran ta sha alwashin gwabza yaƙi da duk ƙasar da ta yi gangancin kai wa Khamenei hari
Syria ta ayyana harshen Kurdanci a matsayin 'harshen ƙasa', sannan ta ba Kurdawa haƙƙin 'yan ƙasa
An buɗe sararin samaniyar Iran bayan rufe shi na wucin-gadi
Trump ya yi barazanar ‘ɗaukar tsattsauran mataki’ idan Iran ta rataye masu zanga-zanga
'Taimako yana zuwa' in ji Trump ga masu zanga-zanga a Iran
Iran ta ce a 'shirye' take ta tattauna da Amurka amma kuma ta 'shirya wa yaƙi'
Kungiyar ta'addanci ta YPG ta ƙwace iko da wani asibiti a Aleppo, ta kori ma'aikatan lafiya
Ma'aikatar Tsaron Syria ta sanar da tsagaita wuta a wasu unguwannin Aleppo
Turkiyya da wasu ƙasashe bakwai suna matsa wa Isra'ila lamba don ɗage takunkuman hana Gaza tallafi
Rundunar hadakar soji da Saudi ke jagoranta ta kai hari kan 'yan-awaren da UAE ke goyon baya a Yemen
Trump ya ce Hamas za ta "ɗanɗana kuɗarta" idan nan da ɗan lokaci ba ta ajiye makamai ba
Hamas ta ce harin Isra'ila ya kashe babban mai magana da yawunta a lokutan yaƙi, Abu Ubaida
Ministan Tsaron Ƙasa na Isra'ila na so a hana kiran sallah a masallatan ƙasar
Iran ta ce ta kama wani jirgin ruwa ɗauke da lita miliyan 4 ta fetur da aka yi fasa-ƙwauri a Gulf
Waiwaye kan 2025: Shekarar kisan ƙare dangi a Gaza da sauran yaƙe-yaƙe a duniya
Yara na mutuwa saboda tsananin sanyi a Gaza