| hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Mayakan Houthi sun ba da alamar dakatar da kai har kan Isra'ila da jiragen ruwa a Tekun Maliya
Mayakan Houthi sun kai hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka kan Isra'ila da jiragen ruwa na ƙasa da ƙasa a Tekunan Maliya da na Aden tun bayan soma yaƙin kisan ƙare dangi na Isra'ila a Gaza.
Mayakan Houthi sun ba da alamar dakatar da kai har kan Isra'ila da jiragen ruwa a Tekun Maliya
Sai dai kawo yanzu 'yan Houthi ba su bayar da wata sanarwa a hukumance cewa hare-haren da suke kai wa yankin sun tsaya cak ba
11 Nuwamba 2025

Mayakan Houthi na Yemen sun ba da alamar dakatar da kai hare-hare kan Isra’ila da kuma jiragen ruwa a Bahar Rum biyo bayan yarjejeniyar tsaigata wuta ta Gaza da aka cim ma, wadda ke tangal-tangal.

A wata wasiƙa da mayakan suka aika wa rundunar sojin Qassam ta Hamas wadda aka yada a daren ranar Litinin, sun bayyana dakatar da kai hare-hare da suke kaiwa cak.

"Muna sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa kana muna bayyana cewa idan abokan gaba suka ci gaba da kai hari Gaza, za mu dawo da ayyukan sojinmu kan Yahudawa, kuma za mu dawo da haramcin zirga-zirgar jiragen ruwa na Isra'ila a Tekun Bahar Rum da kuma na  Larabawa," in ji wasikar.

‘Yan Houthi dai sun yi suna a duniya a lokacin yakin kisan kare dangi da Isra'ila ke yi Gaza inda a bangare guda su kuma suke kai hare-hare kan jiragen ruwa da Isra'ila, wanda suka ce suna yi ne don tilasta wa Isra'ila ta dakatar da yakinta.

Tun da aka cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta wadda ta soma aiki daga ranar 10 ga Oktoba, ƙungiyar ba ta sake ɗaukar alhakin kai wani hari ba.

Kawo yanzu dai mayakan Houthi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan cewa sun dakatar da kai hare-harensu yankin.

Rumbun Labarai
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana