WASANNI
2 minti karatu
Kocin Masar ya nemi a bai wa Salah kyautar Ballon d'Or ta bana
Kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Masar, Hossam Hassan ya ce lokaci ya yi da ƙwallo za ta yi wa Mohamed Salah adalci tahanyar ba wa bamisiren kyautar Ballon d'Or ta bana.
Kocin Masar ya nemi a bai wa Salah kyautar Ballon d'Or ta bana
/ Reuters
6 awanni baya

Yayin da awanni ne suka rage a ayyana wanda ya zama gwarzon ƙwallo ƙafa na duniya a bana, kocin tawagar ƙasar Masar, Hossam Hassan ya yi kira da a girmama tauraron ƙwallo na ƙasar, Mohamed Salah.

Salah na cikin jerin taurarin ‘yan ƙwallon da za a zaɓa don fitar da wanda zai lashe kyautar Ballon d'Or ta shekarar 2025.

Da yake ayyana Salah a matsayin ‘gwarzo abin koyi, Hassan ya ce ɗan wasan da ke buga wa Liverpool ta Ingila, abin koyi ne ga masu neman nasara a fannin ƙwallo a duniya.

A kakar bara, Mohamed Salah dai ya ciyo wa Liverpool ƙwallaye 34 a duka gasanni kuma ya taka rawar gani wajen taimaka wa ƙungiyarsa lashe kofin Firimiya.

Da wuya Salah ya kai labari

A maraicen yau Litinin ne za a gudanar da bikin ba da kyautar gwarazan ƙwallon ƙafa maza da mata a wani ƙasaitaccen biki da za a yi a birnin Paris na Faransa.

Sai dai duka da ƙwazon da ya nuna a bara, masana ƙwallo na ganin zai yi wuya Salah mai shekaru 33 ya kai labari.

Hasali ma, ɗan wasan Paris Saint-Germain ta Faransa, Ousmane Dembele ne ake kyautata zaton zai ɗauki kambin a bana.

Baya ga Dembele, akwai matashin ɗan wasan Barcelona ɗan asalin Saifaniya, Lamine Yamal da kuma wani ɗan wasan Barca ɗan asalin Brazil, Raphinha da ke gaba da Salah a cancantar lashe kyautar.