| hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Gwamnatin Nijar ta rufe kamfanonin tsaro masu zaman kansu 400
Bayanai daga hukumomin Nijar sun ce an ɗauki wannan mataki ne a ƙoƙarin gwamnatin na kawo ƙarshen shekaru da aka shafe na rashin tsari a fannin tsaro da ke da matuƙar muhimmanci.
Gwamnatin Nijar ta rufe kamfanonin tsaro masu zaman kansu 400
Tun ranar 10 ga watan Yunin shekarar 2024 ne ma’aikatar tsaron cikin guda ta janye lasisi aikin kamfanoni uku na samar da tsaro
19 Satumba 2025

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta rufe kamfanonin samar da tsaro masu zaman kansu 400 a lokaci ɗaya ta hanyar wata doka da ministan tsaron cikin gida Manjo Janar Mohamed Toumba ya rattaba wa hannu.

Bayanai daga hukumomin Nijar sun ce an ɗauki wannan mataki ne a ƙoƙarin gwamnatin na kawo ƙarshen shekaru da aka shafe na rashin tsari a fannin tsaro da ke da matuƙar muhimmanci.

Duk da cewa sanarwar ministan ba ta ba da hujja kan rufe kamfanonin ba, kafar watsa labarai ta Actu Niger ta ce an ɗauki matakin domin tsaftace tsarin samar da tsaron ƙasar.

Tun ranar 10 ga watan Yunin shekarar 2024 ne ma’aikatar tsaron cikin guda ta janye lasisi aikin kamfanoni uku na samar da tsaro: Securicom da GADNET Sécurité da kuma Manga Sécurité bayan sun nuna gazawa wajen gudanar da ayyukansu.

A hanlin yanzu waɗannan kamfanonin na cikin kamfanoni 400 da aka rufe har abada.

Yayin da wasu ke ganin wannan matakin a matsayin abin da zai janyo damuwa game da rashin ayyukan yi ga masu gadi, wasu na ganin matakin a matsayin abin da ake buƙata domin magance wani yanayi na rashin tabbas.

Ma’aikata da dama sun soki tsarin albashi da bai kai ya kawo ba da waɗannan kamfanoni ke bayarwa, wanda galibi bai kai 50,000 CFA  ba a ko wane wata, da kuma shafe sa’o’i masu yawa a aiki da rashin kariya kan matsalolin rayuwar yau da kullum.

 Dokar watan Fabrairun shekarar 2025

Domin cike giɓin doka da ke a fannin, ranar 7 ga watan Fabrairun shekarar 2025 ne majalisar ministocin ƙasa ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙasar Janar Abdourahamane Tiani, ta amince da dokar tsara ayyukan kamfanonin tsaro masu zaman kansu.

Kawo yanzu, waɗannan kamfanonin suna aiki ne kan izini na wucin-gadi ba tare da tsare-tsare na sa ido ba. Wannan ne ya sa wasu mutane masu barazana ga tsaron jami’ai suka shiga harkar, in ji rahotanni daga ƙasar.

Dokar ta samar da wani tsari mai ƙarfi ga kamfanoni na tsaro masu zaman kansu, inda ya ba da izinin na shekara biyar da ba za a iya musayarsa ba da wajabta bincike kan ɗabi’un shugabannin kamfanonin da sa ido sosai wajen riƙe makamai da kuma haramta musu yin ayyukan da doka ta ware wa dakarun ƙasar na FDS tare da kafa wata hukuma mai sa ido kan fannin gaba ɗaya.

Baya ga haka dokar ta bai wa dukkan kamfanonin da ke aiki lokacin wa’adin wata shida su cika sharruɗan ko kuma a rufe su

Sabon zamani ga tsaron masu zaman kansu

Wannan tsarin dokar na ranar 18 ga watan Satumbar shekarar 2025 ya ƙunshi jerin kamfanonin da a aka ƙwace rajistarsu daga sanannu irin su Le Bouclier da Tigre Security Group da Lynx Security zuwa waɗanda ba sani ba. Saƙon dokar shi ne: gwamnati na karɓe iko kan wannan muhimmin fannin da bai kamata a bari da matsalolinsa ba

"Duk wanda ya saɓa wa tanade-tanaden wannan dokar za a yake masa hukunci da wannan dokar ta tanada ," in ji dokar.

Wannan matakin zai yi tasiri na tattalin arziƙi da na zamantakewa nan-take. Dubban masu gadi sun fuskantar rashin aikin yi yayin da ya zama dole wa  kamfanonin da dama su nemi sabbin masu kamfanonin tsaro da za su ɗauka domin tabbatar da tsaronsu.

Rumbun Labarai
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan