| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
‘Yan gudun hijira da ke son zuwa Spaniya na bi ta hanyar ta tekun Atlantika daga Yammacin Afirka zuwa Tsibiran Canary, wadda ita ce mafi hatsari a duniya.
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
FILE PHOTO: Kwale-Kwale dauke da 'yan gudun hijira a kan hanyar zuwa Faransa. / Reuters
2 Janairu 2026

An gano gawarwaki bakwai, kuma an ceto mutane 96 bayan da wani jirgin ruwa da ke ɗauke da ‘yan ci-rani ya kife cikin dare a gaɓar tekun Gambia, in ji ma'aikatar tsaro ta Banjul.

Jirgin ruwan, "ana zargin yana ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200", in ji ma'aikatar a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, inda ta ƙara da cewa 10 daga cikin baƙin haure da aka ceto suna cikin mawuyacin hali kuma suna samun kulawar gaggawa ta likita.

Sanarwar ba ta yi bayani kan sauran ‘yan ci-rani da ke cikin jirgin ba yayin da ake ci gaba da ayyukan ceto.

‘Yan gudun hijira da ke son zuwa Sifaniya na bi ta hanyar ta Tekun Atlantika daga Yammacin Afirka zuwa Tsibiran Canary, wadda ita ce mafi hatsari a duniya.

Fiye da ‘yan ci-rani ba bisa ƙa’ida ba su 46,000 sun isa Tsibirin Canary a shekarar 2024, a cewar Tarayyar Turai.

Fiye da mutane 10,000 ne suka mutu a yayin tafiyar zuwa Turai, kuma an samu ƙaruwar kashi 58 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar 2023, a cewar ƙungiyar kare hakkin bil'adama ta Caminando Fronteras.

A watan Agustan 2025, aƙalla mutane 70 ne suka mutu lokacin da wani jirgin ruwa da ake zargi ya tashi daga Gambia ɗauke da baƙin haure ya kife, a daya daga cikin haɗurra mafi muni a cikin 'yan shekarun nan.

Rumbun Labarai
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
'Ba ma so Isra'ila ta kawo mana matsala,' a cewar shugaban Somalia
Rikicin da ke ta’azzara ya tirsasa wa farar-hula fiye da 4,000 tserewa daga Kordofan a Sudan: MDD
Burkina Faso da Mali sun daina bai wa 'yan Amurka bizar zuwa ƙasashensu
China ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na amincewa da yankin Somaliland
Burhan na Sudan ya yi watsi da yarjejeniya ya ce za a cim ma tsagaita wuta ne bayan janyewar tsageru
Nijeriya ta yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin 'yantacciyar ƙasa
Eritrea ta nemi Kwamitin Tsaro na MDD ya yi martani kan amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland
Gwamnatin Nijar ta zartar da dokar tilasta wa 'yan ƙasar shiga aikin soja
Mayaƙan RSF kashe mutum 200 a Darfur na Sudan, ciki har da mata da yara: Likitoci
An karrama 'yar sandar da ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya
Dimokuradiyya ta dawo da ƙarfinta a Somalia bayan shekaru 56
Jamhuriyar Nijar ta dakatar da bai wa 'yan Amurka bizar shiga ƙasarta
Shugaban Burkina Faso Traore ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar ƙawance ta ƙasashen AES
Zargin almundahanar Naira biliyan ɗaya: Nijeriya na tuhumar Malami da ɗansa da laifuka 16
Yadda bijire wa magunguna ke sake taɓarɓarar da ƙoƙarin kawar da cutar malaria a Afirka
Libya ta sanar da zaman makoki na kwana uku bayan mutuwar Babban Hafsan Sojojin kasar
Ƙasashen Ƙawancen Sahel sun kafa tashar watsa labarai a Bamako don haɓaka manufofin yankin
An bayar da shawarar ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa a Ghana