| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
NDLEA ta kama miyagun kwayoyi guda miliyan 12 da dubu dari hudu a Nijeriya
Hukumar ta ce ta kama kwayoyin ne a cikin garin Bauchi da kuma filin jirgin sama na Legas.
NDLEA ta kama miyagun kwayoyi guda miliyan 12 da dubu dari hudu a Nijeriya
NDLEA na yawan kama masu safarar miyagun kwayoyi a Nijeriya. Hoto/NDLEA
23 Yuli 2023

Hukumar da ke yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA ta kama miyagun kwayoyi milyan miliyan sha biyu da dubu dari hudu a Legas da Bauchi.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Lahadi, ta ce kwayar Tramadol da jami’anta suka kama a filin jirgin sama na Legas ta kai ta naira biliyan 3.7.

Hukumar ta ce ta yi wannan kamun tare da hadin gwiwar jami’an kwastam inda suka gano kwayoyi har miliyan biyar da dubu dari da ashirin da biyu da dari tara (5, 122, 900).

Binciken wucin gadi ya nuna cewa an shigar da kwayoyin Nijeriya ne daga kasashen Pakistan da kuma Indiya inda wasu daga cikinsu kuma za a kai su birnin Freetown na Saliyo.

Kwayoyin na Jihar Bauchi da jami’an suka kama sun kai miliyan shida da dubu dari biyu da sittin da biyar da guda tamanin (6,265,080).

Wadanda ake zargi da safarar kwayoyin sun hada da Emmanuel Onyebuchi mai shekara 32 da Uche Iyida mai shekara 33 da Chinedu Ezeanyim mai shekara 32.

NDLEA ta ce an kama su ne a babbar hanyar zuwa Maiduguri a cikin garin Bauchi a ranar Laraba.

A sanarwar da hukumar ta NDLEA ta fitar a ranar Lahadi, ta ce ta kama gawurtaccen mutumin da ya shahara wurin safarar manyan miyagun kwayoyi zuwa Turai, musamman kasar Italiya.

“NDLEA ta kai samame dakin otel dinsa da ke yankin Okota da ke Legas a ranar Juma’a 21 ga watan Yuli a lokacin da yake shirya wani sabon dan aikensa ya hadiya kulli 93 na hodar ibilis da za a kai Italiya,” in ji sanarwar.

Hukumar ta ce Mista Charles Uwagbale ya dauki Uju Dominic mai shekara 32 aiki tun daga Italiya domin ya je Nijeriya ya hadiye kullin hodar ibilis 100 ya koma can Italiyar.

Hukumar ta ce an kama mutumin yana cikin shirin soma hadiye kwayoyin a ranar Juma’a da dare.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta