KASUWANCI
2 MINTI KARATU
Ghana ta kara farashin koko da sama da kaso 60
Gwamnatin kasar ta ce za ta rinka biyan manoman koko cedi 20,943 a maimakon cedi 12,800.
Ghana ta kara farashin koko da sama da kaso 60
Ghana na daga cikin kasashen duniya da ke noma koko. Hoto/Reuters
10 Satumba 2023

Kasar Ghana ta kara kudin da za ta rinka biyan manoman koko da sama da kaso 63.3 cikin 100 ga manomanta.

Wannan na daga cikin matakan da gwamnatin ke dauka na hana fasa kwabrin kokon zuwa kasashen makwafta inda ake sayar da shi a can.

Shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya bayyana cewa manoman za su rinka samun cedi 20,943 wanda kwatankwacin dala 1,837 a duk tan guda.

Gwamnatin ta ce wannan karin zai soma a kakar kokon ta shekarar 2023/2024 wadda ke farawa a watan Satumba.

A baya dai gwamnatin kasar na biyan manoman koko cedi 12,800 a duk tan.

A yayin da yake magana a lokacin kaddamar da sabon farashin, Shugaba Addo ya bayyana cewa wannan shi ne farashi mafi yawa na koko da gwamnati za ta biya manoma koko a sama da shekara 50.

Wannan karin na zuwa ne a daidai lokacin da farashin kokon ya karu a duniya, wanda shi ake amfani da shi wurin yin cakuleti.

Farashin na ta karuwa tun daga karshen watan Yuni, sakamakon cututtukan da tsirrai ke fama da su a Yammacin Afirka ciki har da cutar black pod.

MAJIYA:Reuters
Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci