AFIRKA
3 MINTI KARATU
Turkiyya ta damu game da yarjejeniyar da Ethiopia da Somaliland suka kulla
Ma'aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta bayyana ci gaba da goyon baya da kare martabar 'yancin iyakokin Somalia.
Turkiyya ta damu game da yarjejeniyar da Ethiopia da Somaliland suka kulla
Ma'aikatar Harkokin Wajen ta ce "wannan yanayi na bayyana wajabcin, kamar yadda yake a baya, a warware takaddamar da ke tsakanin Somalia da Somaliland ta hanyar tattaunawa kai-tsaye, kuma hakan zai sasanta 'yan Somaliya." Hoto: TRT World
4 Janairu 2024

Bayan wata yarjejeniya da Ethiopia da Somaliland suka kulla wadda za ta bai wa Ethiopia damar amfani da tashar jiragen ruwan Somaliland da ke Tekun Maliya, Turkiyya ta fitar da sanarwar goyon baya da kare martabar iyakokin Somalia.

"Yarjejeniyar Fahimtar Juna don Hadin Kai da Aiki Tare da aka sanya hannu a kai a Addis Ababa a ranar 1 ga Janairu, 2024 tsakanin Jamhuriyar Ethiopia da Somaliland, ba tare da sani da yardar gwamnatin Somalia ba, na sanya damuwa," in ji Ma'aikatar Harkokin Wajen Turkiyya a wata sanarwa da ta fitar.

Firaministan Ethiopia Abiy Ahmed da Shugaban Kasar Somaliland Muse Bihi Abdi ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar a ranar Litinin.

Bayan kulla yarjejeniyar, Turkiyya ta bayyana goyon bayanta ga hadin kai, 'yancin mulki da kare martabar iyakokin Tarayyar Jamhuriyar Somalia, kamar yadda yake kunshe a wata sanarwa da Ma'aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar a ranar Alhamis din nan, tana mai jaddada muhimmanci aiki da dokokin kasa da kasa kan wannan batu.

Ethiopia da ba ta da iyaka da teku ta sanya hannu da yankin Somaliland da ya balle daga Somalia, don amfani da Tashar Jiragen Ruwa ta Berbera.

A wani bangare na yarjejeniyar, Somaliland ta shirya bayar da fili a tsandauri mai nisan kilomita 20 ga Ethiopia don kafa sansanin sojin ruwa, in ji Abdi a wajen sanya hannun.

Ma'aikatar Harkokin Wajen ta ce "wannan yanayi na bayyana wajabcin, kamar yadda yake a baya, a warware takaddamar da ke tsakanin Somalia da Somaliland ta hanyar tattaunawa kai-tsaye, kuma hakan zai sasanta 'yan Somaliya."

Sanarwar ta kara da cewa "Muna sabunta goyon baya ga duk wani yunkuri da zai kawo wannan tattaunawa."

Yankin Somaliland ya balle daga Somalia sama da shekaru 30 da suka gabata, amma har yanzu Tarayyar Afirka da Majalisar Dinkin Duniya ba su amince da 'yancinsa ba. Har yanzu Somalia na yi wa Somaliland kallon wani bangare nata.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar