| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Shugaban mulkin sojan Nijar ya tattauna da Putin kan haɗin gwiwar tsaro
Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar  Abdourahamane Tiani ya tattauna ta wayar tarho da Vladimir Putin na Rasha inda suka yi magana kan hadin gwiwar tsaro.
Shugaban mulkin sojan Nijar ya tattauna da Putin kan haɗin gwiwar tsaro
Janar Abdourahamane Tchiani ya karbi mulki ne a watan Agustan 2023 bayan juyin mulkin da aka yi wa shugaban Nijar Mohamed Bazoum. / Hoto: Ofishin Shugaban Jamhuriyar Nijar
27 Maris 2024

Shugaban mulkin sojan Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya tattauna ta wayar tarho a ranar Talata da shugaban ƙasar Rasha Vladimir Putin game da "ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro", a cewar sanarwar da aka fitar a hukumance.

Tuni dai ƙasashen biyu suka amince a watan Janairu domin ƙarfafa alaƙar soji a lokacin da Firaministan Nijar Ali Lamine Zeine ya jagoranci wata tawaga zuwa birnin Moscow.

Nijar ta kasance kan gaba a haɗin gwiwa da Ƙasashen Yammacin Duniya wajen yaƙar masu tayar da ƙayar-baya a yankin Sahel, amma ta rungumi Rasha a matsayin sabuwar abokiyar tsaro tun bayan hamɓarar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar a bara.

Shugabanin ƙasashen biyu "sun yi magana kan buƙatar ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin tsaro...domin shawo kan barazanar da ake fuskanta a halin yanzu," in ji sanarwar ta Nijar, wadda aka karanta a gidan rediyon gwamnatin ƙasar.

'Dabarun haɗin kai'

Har ila yau, sun tattauna "ayyukan don haɗin gwiwar ɓangarori da dama da na duniya," in ji sanarwar, ba tare da ba da ƙarin bayani ba kan hakan.

Janar Tiani, wanda ya jagoranci Nijar tun bayan juyin mulkin watan Yuli, ya gode wa Putin saboda "goyon bayan" da Rasha ke ba ƙasar ta yankin Sahel da kuma gwagwarmayar neman ƴancin kan ƙasa.

Tawagar Rasha ma ta ziyarci Nijar a watan Disambar da ya gabata.

Har yanzu dai dakarun Amurka kusan 1,000 na jibge a Nijar duk da cewa an taƙaita zirga-zirgarsu tun bayan juyin mulkin, kuma Washington ta daƙile tallafin da take bai wa gwamnatin.

Nijar ta ayyana daina alaƙar soji da Ƙasashen Yamma

Wata babbar tawagar Amurka ta je Yamai a tsakiyar watan Maris domin sabunta hulɗa da gwamnatin mulkin soja, amma ta ce ba su gana da Tiani ba.

Sabuwar gwamnatin ta yi Allah wadai da haɗin gwiwar soji da Ƙasashen Yamma, tare da yin watsi da alaƙar mulkin mallaka da Faransa.

A baya dai Nijar ta kasance muhimmin sansani ga ƙoƙarin sojojin Faransa na murƙushe ta'addancin da ya samo asali daga yankin Sahel.

Nijar ta bi sahun ƙasashen maƙwabta Mali da Burkina Faso a farkon wannan wata wajen sanar da kafa rundunar haɗin gwiwa da za ta yaƙi hare-haren ta'addancin da aka daɗe ana fama da su a cikin ƙasashen uku.

A watan Janairu ne dai suka bayyana aniyarsu ta ficewa daga ƙungiyar ECOWAS ta ƙasashen yankin Yammacin Afirka.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta