| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
An kashe sojoji 12 da 'yan ta'adda fiye da 100 a wasu hare-hare a Nijar
A harin na farko da aka kai a yammacin yankin Tillaberi a ranar Lahadin da ta gabata, ‘yan ta’addar da suka kai ɗaruruwa sun kashe sojoji biyar tare da jikkata wasu 25 a cewar rundunar.
An kashe sojoji 12 da 'yan ta'adda fiye da 100 a wasu hare-hare a Nijar
Wani hari da aka kai a matsayin ramuwar gayya "ya kashe 'yan ta'adda da dama" da ke da hannu a kisan sojojin, in ji rundunar.
19 Satumba 2024

Wasu jerin hare-hare na kwanton ɓauna da fashe-fashe a Jamhuriyar Nijar sun yi sanadiyar mutuwar sojoji akalla 12 tare da raunata wasu 30, kamar yadda rundunar sojin ta sanar a gidan talabijin na kasar a ranar Laraba.

A harin na farko da aka kai a yammacin yankin Tillaberi a ranar Lahadin da ta gabata, ‘yan ta’addar da suka kai ɗaruruwa sun kashe sojoji biyar tare da jikkata wasu 25 a cewar rundunar.

Hare-haren ramuwa ta ƙasa da na sama sun kashe "yan ta'adda fiye da 100", in ji rundunar, ba tare da bayar da karin bayani kan maharan ba.

A ranar Litinin, a yankin kudu maso yammacin Diffa mai fama da tashin hankali, inda ake yawan kai hare-hare daga kungiyar Boko Haram da kuma reshen kungiyar IS na yammacin Afirka, wasu bama-bamai da aka dasa sun kashe sojoji biyar da ke sintiri, kamar yadda kamfanin dillancin labaran AFP ya rawaito.

Wani harin da aka kai a matsayin ramuwar gayya "ya kashe 'yan ta'adda da dama" da ke da hannu a kisan sojojin, in ji rundunar.

A harin na baya-bayan nan, mayakan sabuwar kungiyar ‘yan adawa da ake kira Patriotic Movement for Freedom and Justice (MPLJ) sun kai wani samame a wani sansanin soji a yankin Agadez da ke arewacin kasar.

Rundunar ta ce sojoji biyu ne suka mutu sannan shida suka jikkata a harin na ranar Talata.

Rundunar ta ƙara da cewa, "nan take aka fara gudanar da bincike domin zaƙulo maharan da suka gudu zuwa kan iyakar kasar Libya."

Kungiyar ta MPLJ ta yi ikirarin cewa ta kashe sojoji 14 da Jandarmomi biyu a harin, sannan ta yi asarar mayaƙanta guda biyu.

Ƙungiyar MPLJ, wadda aka ƙirƙira a watan Agusta, wani reshe ne na kungiyar 'yan tawayen Patriotic Liberation Front (FPL) mai dauke da makamai, wacce ke fafatawa da gwamnatin mulkin soji don sakin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan