| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
Ƙungiyar bayar da agaji ta Libyan Red Crescent ta ce an tura ma’aikatan agajin gaggawa zuwa wurin don ceto waɗanda suka tsira da ɗauko gawawwakin waɗanda suka mutu, da kuma ba da kulawa.
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
Jirgin farko yana ɗauke da 'yan ci-rani 26 daga Bangladesh, inda aka samu huɗu daga cikinsu matattu.
16 Nuwamba 2025

'Yan ci-rani huɗu sun mutu bayan jiragen ruwa guda biyu da ke ɗauke da kusan mutane 100 sun kife a kusa da gaɓar ruwan Al-Khums a arewa maso yammacin Libya, in ji ƙungiyar bayar da agaji ta Libyan Red Crescent.

Ƙungiyar ta ce ta samu rahoto daga daren Alhamis game da jiragen ruwan 'yan gudun hijira guda biyu da suka kife a bakin ruwa a Al-Khums.

Jirgin farko yana ɗauke da 'yan ci-rani 26 daga Bangladesh, inda aka samu huɗu daga cikinsu matattu.

Jirgin na biyu yana ɗauke da mutane 69, ciki har da ‘yan Masar biyu da 'yan Sudan 67, da yara takwas, in ji ƙungiyar ta Red Crescent.

Hukumar ta kara da cewa an tura ma’aikatan agajin gaggawa zuwa wurin don ceto waɗanda suka tsira da ɗauko gawawwakin waɗanda suka mutu, da kuma ba da kulawa.

Ana ganin Libya a matsayin wuri ficewa ga masu son tafiya ci-rani cikin sauƙi ba tare da izini ba da ke ƙoƙarin isa Turai ta haramtacciyar hanya ta hanyar amfani da teku.

Hukumomi na ci gaba da fuskantar ƙaruwar ƙalubalen 'yan ci-rani, yayin da ƙasashen Tarayyar Turai dake bakin Tekun Bahar Rum ke nuna damuwa game da yawan zirga-zirgar 'yan gudun hijira marasa izini zuwa bakin tekunsu.

Kungiyar Kula da ‘Yan Ci-rani ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM) a ranar Laraba ta ce adadin 'yan gudun hijirar da suka mutu yayin ƙoƙarin ketare tsakiyar Tekun Bahar Rum a wannan shekara ya riga ya wuce 1,000.

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi