| Hausa
AFCON 2025
2 minti karatu
Eric Chelle: An zaɓi kocin Nijeriya a matsayin gwarzon koci a zagayen rukuni na AFCON 2025
Daga tawagar Super Eagles ta Nijeriya, Ademola Lookman aka zaɓa a matsayin ɗanwasan tsakiya mai kai hari daga gefen hagu. Lookman ya ci ƙwallo 2 a wasanni 3 da ya buga zuwa yanzu.
Eric Chelle: An zaɓi kocin Nijeriya a matsayin gwarzon koci a zagayen rukuni na AFCON 2025
Eric Chelle ya zama kocin Super Eagles ta Nijeriya ne a Janairun 2025 / Reuters
2 Janairu 2026

Hukumar ƙwallon ƙafar Afirka (CAF) ta ce kocin Nijeriya, Eric Chelle shi ne gwarzon koci a zagayen rukuni na gasar AFCON 2025, yayin da shi ma ɗanwasan Nijeriya, Ademola Lookman ya zama gwarzon ɗanwasan tsakiya da ya fi nuna bajinta.

CAF ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar kan jerin zaratan ‘yanwasa 11 da kocin da ya fi nuna bajinta wajen jagorantar tawagarsa bayan buga jimillar wasanni 36 a zagayen rukuni.

Daga ‘yanwasan akwai golan Masar, Mohamed El Shenawy, da Riyad Mahrez na Aljeriya, da Sadio Mané na Senegal, da Amad Diallo na Ivory Coast.

Masu AlakaTRT Afrika - AFCON 2025: Osimhen da Mane sun ci ƙwallo, yayin da Nijeriya ta yi nasara, Senegal ta yi kunnen doki

Daga tawagar Super Eagles ta Nijeriya, Ademola Lookman aka zaɓa a matsayin ɗanwasan tsakiya mai kai hari daga gefen hagu. Lookman ya ci ƙwallo 2 a wasanni 3 da ya buga zuwa yanzu.

Gwarzon koci

Tawagar Nijeriya ta ƙare zagayen rukuni da maki 9, saboda ta ci duka wasanninta 3, inda ta kara da Tanzania ta ci 2-1, sai Tunisia da ta ci 3-2, sannan Uganda, wadda ta doke da ci 3-1.

Wannan nasara ta Nijeriya, wadda Aljeriya ce kawai cikin sauran ƙasashe 23 ta samu maki 9 a rukuni, ya sa an karrama kocin Super Eagles, Eric Chelle a matsayin gwarzon koci a zagayen.

Chelle ya yi ƙoƙari wajen jagorantar Nijeriya wajen cin jimillar ƙwallaye 8, wanda shi ne mafi yawa da wata tawaga ta ci a gaba ɗaya zagayen.

Kocin na jan ragamar Super Eagles a wata babbar gasa a karon farko, tun bayan da aka ba shi muƙamin jagorantar tawagar a Janairun 2025.

A makon nan ne aka kammala zagayen rukuni na gasar kofin ƙasashen Afirka na AFCON 2025 wanda ake yi a Maroko, inda tawagogi daban-daban suka ƙayatar.