| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari
An bayar da rahoton mummunar arangama tsakanin 'yan tawayen M23 da sojojin gwamnati a wurare da dama a yankin Uvira.
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari
FILE: Fighting between government forces and M23 rebels has displaced people from Uvira town. / AP
3 Janairu 2026

Mummunan tashin hankali ya ɓarke a ranar Asabar tsakanin ‘yantawayen M23 da sojojin da ke goyon bayan gwamnati a wasu garuruwa da ke kewaye da birnin Uvira mai muhimmanci a gabashin Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo, in ji majiyoyi na cikin gida.

Gabashin na Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo mai arziki, wanda ke iyaka da Rwanda da Burundi, ya shafe shekaru 30 yana fama da tashin hankali marar yankewa.

Al'amuran sun kara tsananta tun daga 2021 saboda dawowar kungiyar M23.

Bayan ta kwace manyan biranen gabas biyu, Goma da Bukavu, a karshen bara, kungiyar ta kaddamar da sabon farmaki a watan Disamba a lardin Kivu ta Kudu kuma ta karbe iko ranar 10 ga Disamba da Uvira, birni mai muhimmanci da ke da daruruwan dubban mutane, kusa da Burundi, mai kawance da DRC.

Sulhu da Trump ya shiga tsakani

Kungiyar ta kuma ƙwace iko da wasu yankunan kan iyaka a daidai lokacin da DRC da Rwanda ke sanya hannu kan wata yarjejeniyar sulhu a Washington wacce Shugaba Donald Trump na Amurka ya shiga tsakani wajen ƙulla ta.

Tun daga karfe 3 na dare (0100 GMT), an bayar da rahoton rikici mai zafi tsakanin 'yan tawaye na M23 da Wazalendo (dakarun da ke goyon bayan Kinshasa) da kuma rundunar sojin Jamhuriyar a wasu wurare a yankin Uvira, a lardin Kivu ta Kudu, in ji Kelvin Bwija, mai tsara al'umma na Uvira, kamar yadda ya shaida wa AFP.

Bwija ya ambaci garuruwan Kashombe, Lubanda, Musingwe, Katongo, da Kigongo, waɗanda suke kusan kilomita 10 daga birnin, a matsayin wuraren da ake fafatawa.

'Yanzu haka ana jin karar harbe-harbe a Uvira,' in ji shi.

Wani mazaunin Kigongo, wanda aka same shi ta waya, ya tabbatar wa AFP cewa 'rikicin ya sake barkewa a safiyar yau, ana jin manyan fashe-fashe da harbe-harbe'.

Laftanar Reagan Mbuyi Kalonji, kakakin rundunar sojin Kongo (FARDC) na yankin, ya tabbatar wa AFP da cewa ana 'gabza fada a Kigongo da Katongo, musamman a tsaunukan Kashombe da Lubanda a yankin Uvira'.

Mata da yara sun jikkata

M23 ta sanar a ranar 17 ga Disamba cewa za ta janye daga Uvira, tare da roƙon masu shiga tsakani su tabbatar da kariyar birnin daga tashin hankali da kuma 'sake mayar da sojoji'.

An kuma bayar da rahotanni na rikici mai tsanani a lardin Kivu ta Arewa mai makwabtaka tun ranar Jumma'a, inda aƙalla mutane shida suka rasa rayukansu kuma 41 suka ji rauni a wani harin bam da aka danganta wa rundunar sojin Kongo a karamar hukumar Masisi a lardin Kivu ta Arewa, a cewar majiyoyi na cikin gida.

Médecins Sans Frontières (MSF) ta bayyana a shafukan sada zumunta cewa 'mutane 42, ciki har da yara da mata da dama sun ji rauni daga abubuwa masu kaifi da wasu raunuka, an kawo su Babban Asibitin na Masisi bayan harin jirgin sama a yankin da jama’a ke zama a Masisi'.

MSF ta ƙara da cewa biyu daga cikin waɗannan mutane sun mutu.

Rumbun Labarai
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
'Ba ma so Isra'ila ta kawo mana matsala,' a cewar shugaban Somalia
Rikicin da ke ta’azzara ya tirsasa wa farar-hula fiye da 4,000 tserewa daga Kordofan a Sudan: MDD
Burkina Faso da Mali sun daina bai wa 'yan Amurka bizar zuwa ƙasashensu
China ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na amincewa da yankin Somaliland
Burhan na Sudan ya yi watsi da yarjejeniya ya ce za a cim ma tsagaita wuta ne bayan janyewar tsageru
Nijeriya ta yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin 'yantacciyar ƙasa
Eritrea ta nemi Kwamitin Tsaro na MDD ya yi martani kan amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland
Gwamnatin Nijar ta zartar da dokar tilasta wa 'yan ƙasar shiga aikin soja
Mayaƙan RSF kashe mutum 200 a Darfur na Sudan, ciki har da mata da yara: Likitoci
An karrama 'yar sandar da ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya
Dimokuradiyya ta dawo da ƙarfinta a Somalia bayan shekaru 56
Jamhuriyar Nijar ta dakatar da bai wa 'yan Amurka bizar shiga ƙasarta
Shugaban Burkina Faso Traore ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar ƙawance ta ƙasashen AES
Zargin almundahanar Naira biliyan ɗaya: Nijeriya na tuhumar Malami da ɗansa da laifuka 16
Yadda bijire wa magunguna ke sake taɓarɓarar da ƙoƙarin kawar da cutar malaria a Afirka
Libya ta sanar da zaman makoki na kwana uku bayan mutuwar Babban Hafsan Sojojin kasar
Ƙasashen Ƙawancen Sahel sun kafa tashar watsa labarai a Bamako don haɓaka manufofin yankin
An bayar da shawarar ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa a Ghana