| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Tinubu ya umarci masu riƙe da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara a zaɓen 2027 su ajiye aiki
Umarnin ya shafi duk waɗanda Shugaba Bola Tinubu ya bai wa muƙaman siyasa da ke ƙoƙarin shiga zaɓukan fid da gwani na jam'iyya ko kuma neman tsayawa takara na muƙamai.
Tinubu ya umarci masu riƙe da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara a zaɓen 2027 su ajiye aiki
Umarnin ya shafi dukkan waɗanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa muƙaman siyasa / Reuters
7 awanni baya

Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya ya bai wa duk masu riƙe da muƙaman siyasa da ya naɗa a gwamnatinsa da ke son tsayawa takara zaɓukan shekarar 2027 su ajiye ayyukansu kafin ranar 31 ga watan Maris.

Ranar Talata ne Dewan Goshit, shugaban ofishin watsa labarai da hulɗa da jama’a na ofishin sakataren gwamnatin Tarayya ya bayyana umarnin.

Goshit ya bayyana cewa matakin na shugaban ƙasar ya dace da sashe na 88(1) na dokar zaɓen Nijeriya ta shekarar 2026 da kuma jadawalin da hukumar zaɓen Nijeriya (INEC) ta fitar na zaɓukan fid da gwani na jam’iyyu gabanin zaɓukan shekarar 2027.

Masu AlakaTRT Afrika - Jam’iyyun Adawa a Nijeriya sun yi watsi da Dokar Zabe ta 2026, sun nemi a yi sabon gyara

Umarnin ya shafi duk waɗanda Shugaba Bola Tinubu ya bai wa muƙaman siyasa da ke ƙoƙarin shiga zaɓukan fid da gwani na jam'iyya ko kuma neman tsayawa takara na muƙamai.

Waɗanda lamarin ya shafa sun haɗa da manyan ministoci da ƙananan ministoci da manyan masu ba da shawara na musamman da masu ba da shawara na musamman da dukkan manyan daraktoci da shugabannin hukumomin tarayya da kuma shugabannin kamfanonin gwamnati.

Goshit ya ce ana buƙatar jami’an su miƙa wasiƙun barin aikinsu ga ofishin sakataren gwamnatin tarayya nan da wa’adin da aka bayar.

“Shugaba Tinubu ya jaddada cewa matakin ya zama dole ne domin tabbatar da cikakkiyar biyayya ga dokokin zaɓe da tabbatar da fayyace gaskiya a harkar siyasa da kuma bai wa duk mai son takara dama ta bai-ɗaya gabanin zaɓukan,” in ji sanarwar.

Shugaban ya kuma yi kira ga dukkan jami’an da lamarin ya shafa su bi umarnin sahu da ƙafa, yana mai cewa gwamnatinsa tana jajircewa wajen tabbatar da harkar zaɓen da za a yarda da ita da kuma ƙarfafa cibiyoyin dimokuraɗiyya.