NIJERIYA
1 minti karatu
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Martanin Beijing yana zuwa ne bayan Shugaban Amurka Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin sojin kan Nijeriya kan zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen China, Mao Ning, ta ce ƙasar tana goyon bayan gwamnatin Nijeriya
9 awanni baya

China ta ce tana adawa mai "ƙarfi" ga yunƙurin Amurka na amfani da addini da ‘yancin ɗan’adam "wajen tsoma baki a harkokin Nijeriya” bayan Donald Trump ya yi barazanar yiwuwar kai hari Nijeriya kan zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.

Beijing "tana nuna adawa mai ƙarfi ga ko wace ƙasa [da ke] fakewa da addini da ‘yancin  ɗan’adam a matsayin hujjar tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran ƙasashe da kuma yin barazanar takunkumi da fin ƙarfi kan wasu ƙasashe," in ji mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen China Mao Ning yayin wani taron manema labarai a Beijing.

Masu AlakaTRT Afrika - Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya

"A matsayinmu na muhimmiyar abokiyar hulɗar Nijeriya, China tana goyon bayan gwamnatin Nijeriya wajen jagorantar al'umarta a kan hanyar ci-gaban da ya fi dacewa da yanayin ƙasar, in ji ta.

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin soji  kan Nijeriya ranar Asabar kan zargin yi wa Kiristoci kisan gilla,”  bayan iƙirarin cewa addinin Kiristanci na fuskantar “ƙalubale mai iya shafe shi” a Nijeriya yayin da yake zargin "masu kaifin kishin addinin Musulunci " da "kashe mutane masu yawa."