| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Benin da Nijar sun kori jakadun juna a matakin ramuwar gayya
Zaman tankiya da aka shafe shekaru biyu ana yi tsakanin Benin da Nijar ya kai ga ƙasashen biyu na Yammacin Afirka masu maƙotaka da juna ɗaukar matakin ramuwar gayya ta hanyar korar jakadun juna, kamar yadda ƙasashen biyu suka bayyana ranar Lahadi.
Benin da Nijar sun kori jakadun juna a matakin ramuwar gayya
Niger and Benin have had strained relations for more than two years now. / Reuters
4 Janairu 2026

Ƙasar Benin da maƙociyarta Jamhuriyar Nijar sun kori jakadun juna a wani mataki da masana diflomasiyya ke kallo a matsayin ci gaba da taɓarɓarewar alaƙa da ke tsakanin ƙasashen biyu na Yammacin Afirka waɗanda ke maƙotaka da juna.

Bayanai sun nuna cewa hukumomi a Cotonou ne suka soma ayyana wasu jami’an jakadancin Nijar a Benin a matsayin waɗanda ba sa maraba da ci gaba da zamansu a ƙasar.

Rahotanni sun ce jami’an jakadancin na Nijar sun fice daga ƙasar ranar Alhamis, 1 ga watan Janairu.

Nan-take hukumomi a Yamai suka kori jami’an jakadancin Benin daga Nijar, lamarin da ya sa Benin ta sanar cewa daga ranar Litinin ɗin nan za ta rufe ofishin jakadancinta a Yamai.

Ƙasashen biyu su shafe fiye da shekaru biyu suna zaman doya da manja tun bayan juyin mulkin soji a Nijar da ya kifar da gwamnatin Shugaba Mohamed Bazoum a watan Yulin 2023.

Nijar ta sha yin zargin cewa Benin na son dagula lamura a cikin ƙasarta, wani zargi da mahukunta a birnin Cotonou suka musanta.

Wannan sabuwar dambarwa na zuwa ne wata guda bayan yunƙurin juyin mulki da sojoji suka yi a Benin, wanda shugaban ƙasar ya yi zargin cewa akwai hannun wasu ƙasashen waje, ko da yake bai ambaci sunan kowace ƙasa ba.

Nijar ta yi ƙawance da Burkina Faso da Mali, maƙwabta biyu da suke ƙarƙashin mulkin soji kuma suna ci gaba da aiwatar da manufofin bai-ɗaya na cigaban ƙasashensu, ciki har da ƙaddamar da rundunar soji ta ƙasashen uku da buɗe gidan talbijin da sauransu.

Dukkanin ƙasashen uku sun fita daga Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), wadda Benin ke cikinta, inda suka kafa wata ƙungiyar haɗin kai da ake kira Alliance of Sahel States (AES).

Rumbun Labarai
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
'Ba ma so Isra'ila ta kawo mana matsala,' a cewar shugaban Somalia
Rikicin da ke ta’azzara ya tirsasa wa farar-hula fiye da 4,000 tserewa daga Kordofan a Sudan: MDD
Burkina Faso da Mali sun daina bai wa 'yan Amurka bizar zuwa ƙasashensu
China ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na amincewa da yankin Somaliland
Burhan na Sudan ya yi watsi da yarjejeniya ya ce za a cim ma tsagaita wuta ne bayan janyewar tsageru
Nijeriya ta yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin 'yantacciyar ƙasa
Eritrea ta nemi Kwamitin Tsaro na MDD ya yi martani kan amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland
Gwamnatin Nijar ta zartar da dokar tilasta wa 'yan ƙasar shiga aikin soja
Mayaƙan RSF kashe mutum 200 a Darfur na Sudan, ciki har da mata da yara: Likitoci
An karrama 'yar sandar da ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya
Dimokuradiyya ta dawo da ƙarfinta a Somalia bayan shekaru 56
Jamhuriyar Nijar ta dakatar da bai wa 'yan Amurka bizar shiga ƙasarta
Shugaban Burkina Faso Traore ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar ƙawance ta ƙasashen AES
Zargin almundahanar Naira biliyan ɗaya: Nijeriya na tuhumar Malami da ɗansa da laifuka 16
Yadda bijire wa magunguna ke sake taɓarɓarar da ƙoƙarin kawar da cutar malaria a Afirka
Libya ta sanar da zaman makoki na kwana uku bayan mutuwar Babban Hafsan Sojojin kasar
Ƙasashen Ƙawancen Sahel sun kafa tashar watsa labarai a Bamako don haɓaka manufofin yankin
An bayar da shawarar ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa a Ghana