| Hausa
AFCON 2025
2 minti karatu
AFCON 2025: Za a fara kwata-final yayin da mai masaukin baƙi Maroko ke cikin tsaka-mai-wuya
Magoya bayan Maroko suna buƙatar su ga ƙasar da ke kan gaba a ƙwallon ƙafa a Afirka ta fitar da su kunya, amma ba su gamsu da irin wasan da ƙasar ta buga ba kawo yanzu a gasar ta Cin Kofin Afirka da ke gudana.
AFCON 2025: Za a fara kwata-final yayin da mai masaukin baƙi Maroko ke cikin tsaka-mai-wuya
Achraf Hakimi na Maroko yana jan ƙwallo a wasan zagaye na 16 na Kofin Afirka tsakanin Maroko da Tanzaniya a Rabat, Maroko. / AP
kwana ɗaya baya

Maroko na yunuƙurin neman lashe Kofin Kasashen Afirka a gaban magoya bayansu, amma masu masaukin baki dole su guji jin kunya da faɗuwar baƙar tasa, duk da gagarumar matsin lamba, yayin da za su fuskanci Kamaru a wasan kusa da na ƙarshe ranar Juma'a.

Za a yi wa tawagar Walid Regragui wacce ta gaza idan idan ba ta kai wasan ƙarshe ba a ranar 18 ga Janairu su kuma ɗaga kofin, kuma tambayar ita ce yadda za su yi da irin wannan tsammani da ake musu a cikin kwanaki masu zuwa.

Magoya bayan Maroko suna buƙatar su ga ƙasar da ke kan gaba a ƙwallon ƙafa a Afirka ta fitar da su kunya, amma ba su gamsu da irin wasan da ƙasar ta buga ba kawo yanzu a gasar ta Cin Kofin Afirka da ke gudana.

Tawagar ta Maroko Atlas Lions ta doke Comoros da ci 2-0 a wasansu na farko a ranar 21 ga Disamba, kafin su yi canjaras 1-1 da Mali, a wasan da ‘yan kallo suka ringa yi musu ihu.

"Ba abu ba ne da aka saba ‘yan kallo su kushe mu. Muna so mu samu goyon bayan magoya baya," in ji Kaftin Achraf Hakimi a wani jawabi da ya yi cikin jimami kafin wasan ƙarshe na rukuni da Zambiya.

"Idan magoya baya suna tare da mu za mu iya zama zakarun Afirka tare."

Maroko, waɗanda ke bin bayan Italiya a matsayi na 11 a jerin kasashe na FIFA, sai da ta buƙaci ƙwallon Brahim Diaz bayan hutun rabin lokaci kafin doke tawagar da ba ta taɓa lashe Kofin na Afirka ba.

Cike da ƙwararrun

Abin da aka gani ba shi ne aka yi tsammani daga tawagar da ke cika da 'yan wasa masu baiwa ba, ciki har da muhimman 'yan wasa waɗanda suka shiga tarihin zuwa zagayen kwata final a Gasar Cin Kofin Duniya ta 2022.

Amma Regragui, tsohon ɗan wasan ƙasar wanda aka haifa kuma ya tashi a Faransa, ya jaddada cewa lashe wasa shi ne abin da ya fi muhimmanci — kuma tawagarsa sun kware a hakan, kasancewar ta yi nasara a wasanni 19 a duniya, kafin wasan da aka yi da Mali suka yi kunnen doki.