| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Ƙungiyar Likitocin Sudan ta ce: "RSF ta tattara ɗaruruwan gawawwaki daga tituna da unguwannin birnin, suka binne wasu cikin kabarun bai-ɗaya sannan kuma suka ƙone wasu a wani yunƙurin ɓoye shaidar laifukan da suka aikata wa fararen-hula."
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Ana zargin RSF da aikata laifukan yaƙi a Sudan
9 Nuwamba 2025

Ɗaruruwan fararen-hula ne dakarun RSF suka binne cikin kabarin bai-ɗaya yayin da ƙone wasu a birnin Al-Fasher da ke yammacin Sudan, a ranar Lahadi.

Ƙungiyar Likitocin Sudan ta ce: "RSF ta tattara ɗaruruwan gawawwaki daga tituna da unguwannin birnin, suka binne wasu cikin kabarun bai-ɗaya sannan kuma suka ƙone wasu a wani yunƙurin ɓoye shaidar laifukan da suka aikata wa fararen-hula."

Ta kwatanta binne fararen-hula a matsayin "cikakken kisan kiyashi" kuma ta ce wannan yana "keta dukkan ƙa'idodin duniya da na addini da ke haramta lalata gawawwaki da kuma bayar da dama a binne gawa a cikin mutunci.”

"Halin da ake ciki a Al-Fasher ya wuce matsananciyar masifa ta jin kai; ya zama kisan kiyashi kai tsaye ga rayuwa da mutuncin ɗan adam a cikin wani yanayi na shiri da duniya ta yi wanda kusan ya zama nau'i na haɗin baki," in ji bayanin.

'Ba za a iya goge laifuka ba'

"Ba za a iya goge laifukan RSF ta hanyar binne ko ƙone gawawwaki ba," in ji ƙungiyar likitocin, tana kiran al'ummar duniya da su ɗauki mataki na gaggawa don kaddamar da binciken duniya mai zaman kansa game da mummunan zalunci kan fararen hula a Al-Fashir.

A ranar 26 ga Oktoba, RSF ta ƙwace iko da Al-Fasher, babban birnin Arewacin Darfur, kuma ƙungiyoyi cikin gida da na duniya sun ce an aikata kisan ƙabilanci tare da gargaɗin cewa harin zai iya ƙarfafa rarrabuwar ƙasa ta wurare.

Tun 15 ga Afrilun 2023, sojin Sudan da RSF suke yaƙi a tsakaninsu inda aka kasa yin sulhu zuwa yanzu. Rikicin ya kashe dubban mutane kuma ya tilasta wa miliyoyin yin hijira daga gidajensu.

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD