| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Shugaban ƙasar Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Touadera ya samu nasarar yin wa’adi na uku
Hukumar zaɓe ta ce Faustin-Archange Touadera ya samu kashi 76.15 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen watan jiya.
Shugaban ƙasar Jamhuriyar Tsakiyar Afirka Touadera ya samu nasarar yin wa’adi na uku
An fara zaɓar sa a shekarar 2016 kuma aka sake zaɓar sa a karo na biyu a shekarar 2020 / Reuters / Reuters
6 Janairu 2026

Shugaba Faustin-Archange Touadera ya lashe wa'adi na uku a kan mulki a JJamhuriyar Tsakiyar Afirka, bisa ga sakamakon wucin-gadi da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta fitar.

Hukumar ta ce Touadera ya samu kashi 76.15 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen watan jiya.

An fara zaɓarsa a shekarar 2016 kuma aka sake zaɓarsa a karo na biyu a shekarar 2020 da kashi 53.16 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa a zagaye na farko.

Jefa kuri'ar ya biyo bayan zaɓen raba-gardama kan kundin tsarin mulki a shekarar 2023 wanda ya cire iyakance wa'adin mulkin shugaban ƙasa kuma ya tsawaita kowane wa'adi zuwa shekaru bakwai, wanda hakan ya bai wa Touadera damar tsayawa takara a karo na uku.

Tsohon malamin lissafi mai shekaru 68 ya yi kamfe ne kan abin da ya bayyana a matsayin ci gaba a fannin tsaro.

Masu sa ido na ƙasashen duniya, ciki har da Tarayyar Afirka da MINUSCA, sun bayyana zaɓen a matsayin wanda ya gudana cikin lumana, duk da ci gaba da rashin tsaro a sassan gabashin kasar.

Duk da haka, ƙawancen ‘yan adawa, Jam'iyyar RBDC, ya ƙaurace wa zaɓen, yana mai cewa ba a yi adalci ba.

'Yan takara da dama da suka shiga zaɓen, ciki har da tsoffin firaminista Anicet-Georges Dologuele da Henri-Marie Dondra, sun zargi hukumomi da sanya takunkumin yaƙin neman zaɓe, ciki har da taƙaita tafiye-tafiye zuwa yankuna da larduna.

Kotun Tsarin Mulki na da har zuwa ranar 20 ga Janairu don tabbatar da sakamakon ko yanke hukunci kan duk wani ƙalubale.

Duk da cewa 'yan adawa sun yi zargin cewa an tafka maguɗi, ya zuwa yanzu ba a bayar da rahoton wani mummunan tashin hankali bayan zaɓen ba.

 

Rumbun Labarai
Kotun Kolin Guinea ta tabbatar da Doumbouya a matsayin wanda ya lashe zaben kasar
Benin da Nijar sun kori jakadun juna a matakin ramuwar gayya
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
'Ba ma so Isra'ila ta kawo mana matsala,' a cewar shugaban Somalia
Rikicin da ke ta’azzara ya tirsasa wa farar-hula fiye da 4,000 tserewa daga Kordofan a Sudan: MDD
Burkina Faso da Mali sun daina bai wa 'yan Amurka bizar zuwa ƙasashensu
China ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na amincewa da yankin Somaliland
Burhan na Sudan ya yi watsi da yarjejeniya ya ce za a cim ma tsagaita wuta ne bayan janyewar tsageru
Nijeriya ta yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin 'yantacciyar ƙasa
Eritrea ta nemi Kwamitin Tsaro na MDD ya yi martani kan amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland
Gwamnatin Nijar ta zartar da dokar tilasta wa 'yan ƙasar shiga aikin soja
Mayaƙan RSF kashe mutum 200 a Darfur na Sudan, ciki har da mata da yara: Likitoci
An karrama 'yar sandar da ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya
Dimokuradiyya ta dawo da ƙarfinta a Somalia bayan shekaru 56
Jamhuriyar Nijar ta dakatar da bai wa 'yan Amurka bizar shiga ƙasarta
Shugaban Burkina Faso Traore ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar ƙawance ta ƙasashen AES
Zargin almundahanar Naira biliyan ɗaya: Nijeriya na tuhumar Malami da ɗansa da laifuka 16
Yadda bijire wa magunguna ke sake taɓarɓarar da ƙoƙarin kawar da cutar malaria a Afirka