| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
Tun bayan ɗaukar makamai a 2021, ƙungiyar M23 ta ƙwace iko da gabashin DRC da ke da albarkatun ƙasa, wanda suka dinga janyo rikicin jinƙai a yankin.
DRC ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a wata ɗaya da ya gabata
Rikicin gabashin DRC ya samo asali daga burbushin kisan kiyashin Rwanda na 1994 da kuma kokarin kwace albarkatun kasa na DRC. / AP
2 Janairu 2026

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo (DRC) ta zargi Rwanda da kashe fararen-hula fiye da 1,500 a gabashin DRC tun farkon Disamba, lokacin da 'yantawayen M23 suka ƙaddamar da sabbin hare-hare.

'Yan kwanaki bayan da gwamnatin DRC da Rwanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da Amurka ta shiga tsakani a ranar 4 ga Disamba, M23 ta ƙwace babban birnin Uvira, abin da ya sa dubban mutane suka tsere zuwa kan iyaka suna shiga Burundi.

DRC ta zargi Rwanda da goyon bayan 'yantawayen M23. Amma Rwanda ta musanta zargin.

"Alƙaluman wucin-gadi da aka fitar na fararen-hula da suka mutu sakamakon hare-haren Rwanda da aka kai da bama-bamai da jiragen yaƙi marasa matuƙa tun farkon watan Disamba sun nuna kisan fiye da 1,500," a cewar wata sanarwa da DRC ta fitar a ranar Laraba.

Da take Allah wadai da "aikin zalunci da Rwanda ta aikata", DRC ta kuma zargi Kigali da aika "sabbin bataliyoyin Rwanda guda uku" zuwa gabashin lardin Kudancin Kivu, don ci gaba isa ga "yankin Kalemie mai mahimmanci" a lardin kudu maso gabashin Tanganyika da ake haƙar ma'adinai.

Masu AlakaTRT Afrika - Congo DRC da Rwanda sun sa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya don kawo ƙarshen yaƙi

Idan M23 ta yi isa zuwa kudu zuwa Tanganyika, ƙungiyar mai ɗauke da makamai za ta samu gindin zama a arewa maso gabashin yankin da aka fi sani da lardin Katanga, wato cibiyar hakar ma'adinai ta DRC.

Tun bayan sake ɗaukar makamai a shekarar 2021, ƙungiyar M23 ta ƙwace yankunan gabashin DRC mai arzikin ma'adinai, inda ta kori dubban mutane daga gidajensu, ta kuma haifar da rikicin jinƙai mai tsanani.

Bayan ƙaddamar da sabbin hare-hare a ranar 2 ga Disamba, bayan dakatarwar watanni shida, ƙungiyar masu ɗauke da makamai ta kwace Uvira a ranar 10 ga Disamba, tare da ƙwace iko da kan iyakar ƙasar da Burundi, ƙawar DRC.

Bayan da Washington ta zargi Rwanda da karya yarjejeniyar zaman lafiya, wadda shugaban Amurka Donald Trump ya kira a matsayin yarjejeniyar "mu'ujiza", duk da harin M23, ƙungiyar ta ce a ranar 17 ga Disamba za ta janye daga birnin mai dubban mutane.

Amma Washington da DRC sun nuna shakku kan sahihancin sanarwar M23, yayin da majiyoyin yankin suka shaida wa AFP a ranar Alhamis cewa mambobin M23 da jami'an 'yansanda sun tsaya sun zauna a Uvira.

A farkon makon nan, sojojin DRC sun ce sun sake ƙwace wasu matsugunan da ke kewaye da Uvira bayan "arangama ta ɓarke."

Ƙwace garin ya zo ne kusan shekara guda bayan da M23 ta ƙwace manyan biranen gabashin Goma da Bukavu, manyan biranen lardunan Arewa da Kudancin Kivu.

A cewar Majalisar Dinkin Duniya, fiye da mutane 80,000 sun tsere zuwa Burundi bayan sake danna kai na M23, wanda ya kuma raba aƙalla mutane rabin miliyan da muhallansu a Kudancin Kivu kawai.

Rumbun Labarai
Sabon rikici ya ɓarke tsakanin sojojin DRC da 'yantawayen M23 a kusa da wani babban gari
Jirgin ruwa ɗauke da ‘yan ci-rani fiye da 200 ya kife a gaɓar tekun Gambia
'Ba ma so Isra'ila ta kawo mana matsala,' a cewar shugaban Somalia
Rikicin da ke ta’azzara ya tirsasa wa farar-hula fiye da 4,000 tserewa daga Kordofan a Sudan: MDD
Burkina Faso da Mali sun daina bai wa 'yan Amurka bizar zuwa ƙasashensu
China ta yi Allah wadai da matakin Isra'ila na amincewa da yankin Somaliland
Burhan na Sudan ya yi watsi da yarjejeniya ya ce za a cim ma tsagaita wuta ne bayan janyewar tsageru
Nijeriya ta yi watsi da amincewar da Isra’ila ta yi wa Somaliland a matsayin 'yantacciyar ƙasa
Eritrea ta nemi Kwamitin Tsaro na MDD ya yi martani kan amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland
Gwamnatin Nijar ta zartar da dokar tilasta wa 'yan ƙasar shiga aikin soja
Mayaƙan RSF kashe mutum 200 a Darfur na Sudan, ciki har da mata da yara: Likitoci
An karrama 'yar sandar da ta ƙi karɓar cin hancin dala 50,000 a Zambiya
Dimokuradiyya ta dawo da ƙarfinta a Somalia bayan shekaru 56
Jamhuriyar Nijar ta dakatar da bai wa 'yan Amurka bizar shiga ƙasarta
Shugaban Burkina Faso Traore ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar ƙawance ta ƙasashen AES
Zargin almundahanar Naira biliyan ɗaya: Nijeriya na tuhumar Malami da ɗansa da laifuka 16
Yadda bijire wa magunguna ke sake taɓarɓarar da ƙoƙarin kawar da cutar malaria a Afirka
Libya ta sanar da zaman makoki na kwana uku bayan mutuwar Babban Hafsan Sojojin kasar
Ƙasashen Ƙawancen Sahel sun kafa tashar watsa labarai a Bamako don haɓaka manufofin yankin
An bayar da shawarar ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa a Ghana