| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Dakarun Nijeriya sun kubutar da wani Kanal mai ritaya da aka yi garkuwa da shi a jihar Filato
An yin garkuwa da babban jami'in mai ritaya a safiyar ranar 5 ga Janairun 2026 da misalin ƙarfe 00:45 daga gidansa da ke daura da Cocin Salvation Army da ke kan titin Rukuba, karamar hukumar Bassa.
Dakarun Nijeriya sun kubutar da wani Kanal mai ritaya da aka yi garkuwa da shi a jihar Filato
Sojojin sun ceto wani Kanal daga hannun 'yan bindiga a Filato / Nigerian army
6 Janairu 2026

Dakarun Sojin Nijeriya da ke kai Farmakan ‘Enduring Peace’ sun kubutar da wani babban jami’in soji, Kanal Ajanaku mai ritaya, bayan garkuwa da shi da wasu ‘yan bindiga suka yi a yankin Karamar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.

An yin garkuwa da babban jami'in mai ritaya a safiyar ranar 5 ga Janairun 2026 da misalin ƙarfe 00:45 daga gidansa da ke daura da Cocin Salvation Army da ke kan titin Rukuba, karamar hukumar Bassa.

Bayan samun kiran gaggawa, sojojin Sashe na 1 da na 3, da ke kai Farmakan ‘ENDURING PEACE’ sun yi gaggawar fita tare da tare da bin diddigin inda suka nufa a hanyar filin shakatawa na Wildlife Park.

Sojojin, tare da hadin gwiwar Sashen Leken Asiri na Rundunar Sojin Kasa ta Nijeriya, da kuma 'yan banga na yankin, sun ci gaba da gudanar da bincike da ceto mai zurfi, suna farautar maboyar masu laifi a cikin kogo da tsaunukan duwatsu da ke yankin.

Daga baya a wannan ranar, da misalin ƙarfe 14:00, masu garkuwar sun tuntubi matar jami'in mai ritaya da aka yi garkuwa da shi, kuma suka nemi a biya su fansar Naira Miliyan Ɗari Biyu (₦200,000,000.00).

Bayan sun lura da yawan kasancewar sojoji da matsin lamba daga sojojin, masu garkuwar sun yi barazanar kashe wanda suka yi garkuwan da shi idan ba a dakatar da ayyukan bincike ba.

Saboda haka, sojoji suka koma gudanar da ayyukansu a ɓoye, wanda ya kai ga nasarar ceto Kanal Ajanaku mai ritaya da misalin ƙarfe 17:30 a ranar 5 ga Janairun 2026 a gefen Rafiki Axis, ƙaramar hukumar Bassa, jihar Filato, ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

A yanzu ana ci gaba da duba lafiyar jami’in sojan da aka kubutar kuma yana cikin yanayi mai kyau, a cewar rundunar sojin ƙasar. Ta kuma ce daga baya zai bayar da bayanan yadda za a kamo ‘yan ta’addar da suka gudu.

A halin yanzu, sojojin na ci gaba da kai hare-hare a cikin dazuzzukan da ke kewaye don kama masu garkuwa da mutanen da suka gudu da kuma wargaza hanyoyin sadarwarsu yayin aikata laifuka.

Rundunar Sojojin Najeriya, ta hanyar Farmakan ‘ENDURING PEACE’, ta sake jaddada kudirinta na kare rayuka da dukiyoyi kuma za ta ci gaba da hana masu aikata laifuka 'yancin yin aiki a duk fadin yankin.

Rumbun Labarai
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje