AFIRKA
3 MINTI KARATU
Algeria za ta sa ido don hana kudin-cizo shiga kasarta 'daga Faransa'
Ma'aikatar, ƙarƙashin haɗin gwiwa da hukumomi da dama sun ƙaddamar "da matakan sa ido da lura don hana shigar kuɗin-cizon."
Algeria za ta sa ido don hana kudin-cizo shiga kasarta 'daga Faransa'
Kuɗin-cizo wasu ƙananan ƙwari ne da suka fi maƙalewa a jikin katako ko shimfiɗar kwana. Hoto: OTHERS
5 Oktoba 2023

Hukumomin Aljeriya sun sanar da cewa suna ɗaukar ƙwararan matakan lafiya a kan iyakokin ƙasar don hana kuɗin-cizo shiga ƙasar daga Faransa, ƙasar da a kwanan nan suka mamaye biranenta.

A wata sanarwa da Ma'aikatar Lafiya ta Aljeriya ta fitar ranar Alhamis ta sanar da "ɗaukar ƙwararan matakan lafiya don hana yaɗuwar duk wata annoba."

Ma'aikatar, ƙarƙashin haɗin gwiwa da hukumomi da dama sun ƙaddamar "da matakan sa ido da lura don hana shigar kuɗin-cizon."

A cewar ma'aikatar, matakan sun haɗa da "bin ƙwaƙƙwafin hanyoyin lafiya da feshin maganin ƙwari a jiragen sama da na ruwa da motocin sufuri musamman a lokutan da ma'aikatan cibiyoyin kan iyaka suka lura da wata barazana. "

Ministan Lafiya na Aljeriya Abdelhak Saihi ya ƙaryata labarin da aka yaɗa ranar Talata cewa kuɗin-cizo sun shiga ƙasar ta Arewacin Afirka.

Tashin hankalin da ya samu Faransa

Kuɗin-cizo sun yaɗu a biranen ƙasar Faransa, lamarin da ya jawo fargaba a tsakanin ƴan Aljeriya kan yiwuwar ƙwarin za su iya shiga ƙasarsu, ganin yawan mutanen da ke kai kawo a tsakanin ƙasashen biyu.

A ranar Talata ne Ministan Lafiya na Faransa Aurelien Rousseau ya nemi al'umma da ka da su ta da hankulansu a kan yaduwar kuɗin cizon.

A farkon makon nan ne gwamnatin Faransa ta sha alwashin ɗaukar matakai tare da "tabbatar da cewa za ta kare" al'ummarta daga annobar kuɗin-cizon.

Gomman bidiyoyin da aka wallafa a shafukan sada zumunta da dama sun nuna yadda kuɗin-cizon ke yaɗuwa a motocin bas-bas da jiragen ƙasa da filayen jiragen sama da sauran wuraren taruwar al'umma a Paris.

Gasar Wasannin Olympic

Annobar yaɗuwar kuɗin-cizon na zuwa ne a lokacin da Faransa ke shirye-shiryen karɓar baƙuncin Gasar Wasannin Olympic ta 2024 a Paris.

Kuɗin-cizo wasu ƙananan ƙwari ne da suka fi maƙalewa a jikin katako ko shimfiɗar kwana, kuma sukan hau jikin mutane ko dabbobi su sha jini, sannan cizonsu yana da ƙaiƙayi sosai, kuma suna saurin hayayyafa a cikin gidaje ko wuraren da mutane ke zama.

MAJIYA:AA
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar