KASUWANCI
2 minti karatu
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da rahotannin da ke cewa kamfanin zai rufe sashin sarrafa mai na kamfanin har na tsawon watanni.
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Matatar man Dangote ta ƙaryata rahotannın rufe sashen sarrafa man fetur din kamfanin
8 Satumba 2025

Matatar mai ta Dangote ta ƙaryata rahoton da ke cewa za ta iya rufe matatar mai na tsawon watanni biyu zuwa uku, kamar yadda mai magana da yawun rukunin kamfanin na Dangote Anthony Chiejina ya bayyana rahoton a matsayin "tsantsar ƙarya" wadda ba ta da tushe balle makama.

A wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fitar, ya bayyana cewa, ‘‘akwai yiwuwar rufe sashen matatar man kamfanin wadda ke samar da ganga 650,000 a kowace rana tsawon watanni biyu zuwa uku saboda yin wasu gyare-gyare, yana mai ambato shawarar da masana'antar IIR Energy da ke sa ido kan makamashi ta bayar.

A cewar rahoton, tun daga ranar 29 ga watan Agusta aka yi ikirarin rufe sashen matatar man bayan da aka samu matsala ta kwararar mai daga ɓangaren tace man masana’antar.

Kazalika rahoton ya ƙara da cewa, matatar za ta yi ƙoƙarin sake soma aikin tace mai na ganga 204,000 a kowace rana daga 20 ga watan Satumba, amma manyan gyare-gyare da kuma sauya wasu kayan aiki ka iya sanyawa a rufe ta tsawon wasu watanni.

Da yake mayar da martani kan rahoton, Anthony Chiejina, ya bayyana ikirarin a matsayin "labarin karya," kana ya aza ayar tambaya kan dalilin da ya sa Reuters zai yi amfani da kalmar ‘yiwuwa’ idan har yana da tabbaci kan shirin rufewar matatar, kamar yadda ya shaidawa jaridar Punch a ranar Lahadi.

Kamfanin dillancin labaran Reuters dai ya bayar da rahoton cewa ana sa ran rufe sashen kamfanin Dangote na RFCCU na aƙalla makonni biyu.

Matatar mai ta Dangote, wadda ta soma sarrafa ɗanyen mai a watan Janairun 2024, ta sauƙaƙa harkokin mai na cikin gida tare da da kawo cikas ga harkar cinikayyar fitar da man fetur daga ƙasashen Turai zuwa yamma.

Kazalika kasuwancin fitar da man fetur daga ƙasashen Turai da Birtaniya zuwa Nijeriya ya ragu daga ganga kusan 200,000 a shekarar 2024 zuwa kusan 120,000 a watanni shidan farko na wannan shekara ta 2025, a cewar kafar tattara bayanai ta Kpler.

Haka kuma, matatar ta yi jigilar hanyoyin man fetur guda biyu zuwa gabar tekun Gabas ta Amurka, kuma ana sa ran isarsu yankin New York nan gaba a cikin wannan wata,

Hakan na zama wani gagarumin ci gaba ne, inda masu sa ido kan masana'antu ke bibiyar lokacin da matatar za ta samar da mai da zai yi gogayya da na Amurka.

Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji