| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya - Ministan Tsaron Nijeriya
Badaru ya fadi hakan ne a yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida a wani taron manema labarai na Bikin Ranar Tunawa da Dakarun Soji na 2026 da aka yi a ranar Laraba a Abuja.
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
Ministan Tsaro na Nijeriya, Badaru Abubakar
12 Nuwamba 2025

Ministan Tsaron NIjeriya, Mohammed Badaru Abubakar ya ce gwamnatin tarayya za ta kare duk wani jami’in rundunar tsaron kasar da ke aikinsa bisa doka da oda.

Badaru ya fadi hakan ne a yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida a wani taron manema labarai na Bikin Ranar Tunawa da Dakarun Soji na 2026 da aka yi a ranar Laraba a Abuja.

Minista Badaru ya yi wadannan kalamai ne bayan wata sa’insar da ta faru a ranar Talata tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da wani sojan ruwa, Laftanal Kanal A.M Yerima a kan wani fili a Abuja.

'Yan Nijeriya na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu sakamakon sa-in-sar da Ministan Babban Birnin Tarayya Nyesom Wike ya yi da wani matashin soja mai suna A.M. Yerima a yayin duba wani fili da ya yi zargin cewa ba a bi doka wajen mallakarsa ba.

Taƙaddamar ta fara ne a lokacin da Minista Wike ya yi tattaki da kansa zuwa filin, wanda mallakin wani tsohon babban hafsan sojin ruwa ne da aka jibge sojoji a cikinsa.

Wike ya nuna ɓacin ransa bayan sojan ya hana shi shiga filin, inda ya riƙa zagin sojan, matakin da wasu ke ganin bai dace ba.

Da yake magana kan lamarin, Badaru ya ce Ma’aikatar Tsaro tana sane da lamarin kuma za ta tabbatar da cewa an bai wa dukkan jami’ai kariya a yayin da suke gudanar da ayyukansu.

“A ma’aikatar nan, dama cikin rundunar soji, za mu kare dukkan jami’ai da ke bakin aiki a ko yaushe,” ya ce.

“Muna nazarin wannan batun, kuma ina tabbatar muku cewa duk wani jami'i da yake aikinsa bisa ka'ida za a ba shi kariya. Ba za mu bari wani abu ya faru da shi ba matukar a kan aikinsa yake kuma yana yin aikin yadda ya kamata.”

Sai dai ministan bai fayyace bayani a kan binciken da ake yi kan lamarin ba.

Rumbun Labarai
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka