| hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000 bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Wani jami’in Ƙungiyar Tarayyar Turai ya ce ƙungiyar za ta yi tayin horas da ‘yan sandan Falasɗinu a wani ɓangare na matakin ƙoƙarin samar da tsaro mai ɗorewa a yankin.
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000   bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000 bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
19 Nuwamba 2025

Ƙungiyar Tarayyar Turai tana son ta horas da ‘yan sanda Falasɗinawa 3,000 a Gaza a ƙarƙashin wani shiri mai kama da wanda take aiwatarwa a Gaɓar Yamma Da Kogin Jordan  da aka mamaye, kamar yadda wani jami’i ya bayyana ranar Laraba.

Za a "buƙaci samar da zaman lafiya a Gaza da muhimmiyar rundunar ‘yan sanda " idan wannan yarjejeniyar tsagaita wutar ta ɗore, in ji jami’in, wanda aka sakaye sunansa.

Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ya kaɗa ƙuri’ar amincewa da ƙudurin da Amurka ta tsara na ƙarfafa shirin Trump a Gaza — wanda ya ba da damar ɗorewar yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da ƙungiyar gwagwarmayar Falasɗinawa Hamas tun ranar 10 ga watan Oktoba.

Shirin zaman lafiyar ya ba da izinin samar da runduna na ƙasa da ƙasa da za ta yi aiki da Isra’ila da Masar da kuma sabon rundunar ‘yan sandan Falasɗinawan da aka horas da wajen kare kan iyakokin da kuma Gaza da aka ɗauke wa sojoji.

Ƙungiyar Tarayyar Turai dai da ƙyar take iya tasiri kan yaƙin da Amurka ta shafe shekaru biyu tana yi a kan Gaza sakamakon rarrabuwar kai a tsakanin ƙasashen da ke goyon bayan Tel Aviv da kuma waɗanda ke goyon bayan Falasɗinawa.

Domin ta matsu da sake samun ƙarfin faɗa aji a yankin, Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ce za ta gabatar da shirin horas da ‘yan sanda Falasɗinawa — waɗanda ba su da alaƙa da Hamas — a wani banagre na ƙoƙarin sake mayar da tsaro mao ɗorewa a yankin.

Gyara a gwamnatin Falasɗinu

Har yanzu kimanin ‘yan sanda 7,000 a Gaza sun asmaun albashinsu ne daga gwamnatin tarayyar Nijeriya wanda ke mulkan Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye, kamar yadda jami’in ya bayyana.

Da yawa daga cikinsu sun yi ritaya ko kuma ba sa iya aiki, amma za a iya horas da mutum 3,000, a cewarsa.

Za a yi horaswar ne a wajen Gaza, in ji shi.

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ɗauki nauyin horas da ‘yan sanda a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan tun shekarar 2006, da kasafin kudin da ya kai yuro miliyan 13 (misalin dala miliyan 15).

Ministocin Harkokin Wajen Ƙasashen Tarayyar Turai za su tattauna shawarar horaswar ranar Alhamis a Brussels.

Ƙungiyar za ta kuma karɓi baƙuncin wani taron masu ba da tallafi wa Falasɗinu a ranar, wanda zai tattara wakilai 60, ciki har da na ƙasashen Larabawa — amma ban da Isra’ila.

Taron zai bai wa mahalarta damar "tattauna" iya ci-gaban da aka samu kan sauyi a gwamnatin Falasɗinawa, in ji jami’in.

Ƙungiyar Tarayyar Turai ita ce ta babbar mai tamaka wa gwamnatin Falasɗinawa,kuma ta gindaya sharaɗin cewa duk wani tallafi na gaba kawo gyara wanda take ganin yana da muhimmanci ga gwamnatin falasɗinawa ta taka tata rawar wajen samar da mafita ta ƙasashe biyu ga rikicin Isra’ila da Falasɗinu wanda Turai ta daɗe tana goyon baya.

 

Rumbun Labarai
Isra'ila ta kashe fararen-hula 114 a Lebanon bayan saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta: MDD
Mayakan Houthi sun ba da alamar dakatar da kai har kan Isra'ila da jiragen ruwa a Tekun Maliya
Israila ta rushe gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da sabon hari a Khan Younis
Trump ya ce “nan ba da jimawa ba” za a samar da dakarun tsaro na ƙasa da ƙasa a Gaza
Sau 27 Yahudawa 'yan-kama-wuri-zauna suka kutsa Masallacin Kudus a watan da ya wuce - Falasdinu
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta