| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000 bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Wani jami’in Ƙungiyar Tarayyar Turai ya ce ƙungiyar za ta yi tayin horas da ‘yan sandan Falasɗinu a wani ɓangare na matakin ƙoƙarin samar da tsaro mai ɗorewa a yankin.
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000   bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000 bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza / Reuters
19 Nuwamba 2025

Ƙungiyar Tarayyar Turai tana son ta horas da ‘yan sanda Falasɗinawa 3,000 a Gaza a ƙarƙashin wani shiri mai kama da wanda take aiwatarwa a Gaɓar Yamma Da Kogin Jordan  da aka mamaye, kamar yadda wani jami’i ya bayyana ranar Laraba.

Za a "buƙaci samar da zaman lafiya a Gaza da muhimmiyar rundunar ‘yan sanda " idan wannan yarjejeniyar tsagaita wutar ta ɗore, in ji jami’in, wanda aka sakaye sunansa.

Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ya kaɗa ƙuri’ar amincewa da ƙudurin da Amurka ta tsara na ƙarfafa shirin Trump a Gaza — wanda ya ba da damar ɗorewar yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da ƙungiyar gwagwarmayar Falasɗinawa Hamas tun ranar 10 ga watan Oktoba.

Shirin zaman lafiyar ya ba da izinin samar da runduna na ƙasa da ƙasa da za ta yi aiki da Isra’ila da Masar da kuma sabon rundunar ‘yan sandan Falasɗinawan da aka horas da wajen kare kan iyakokin da kuma Gaza da aka ɗauke wa sojoji.

Ƙungiyar Tarayyar Turai dai da ƙyar take iya tasiri kan yaƙin da Amurka ta shafe shekaru biyu tana yi a kan Gaza sakamakon rarrabuwar kai a tsakanin ƙasashen da ke goyon bayan Tel Aviv da kuma waɗanda ke goyon bayan Falasɗinawa.

Domin ta matsu da sake samun ƙarfin faɗa aji a yankin, Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ce za ta gabatar da shirin horas da ‘yan sanda Falasɗinawa — waɗanda ba su da alaƙa da Hamas — a wani banagre na ƙoƙarin sake mayar da tsaro mao ɗorewa a yankin.

Gyara a gwamnatin Falasɗinu

Har yanzu kimanin ‘yan sanda 7,000 a Gaza sun asmaun albashinsu ne daga gwamnatin tarayyar Nijeriya wanda ke mulkan Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye, kamar yadda jami’in ya bayyana.

Da yawa daga cikinsu sun yi ritaya ko kuma ba sa iya aiki, amma za a iya horas da mutum 3,000, a cewarsa.

Za a yi horaswar ne a wajen Gaza, in ji shi.

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ɗauki nauyin horas da ‘yan sanda a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan tun shekarar 2006, da kasafin kudin da ya kai yuro miliyan 13 (misalin dala miliyan 15).

Ministocin Harkokin Wajen Ƙasashen Tarayyar Turai za su tattauna shawarar horaswar ranar Alhamis a Brussels.

Ƙungiyar za ta kuma karɓi baƙuncin wani taron masu ba da tallafi wa Falasɗinu a ranar, wanda zai tattara wakilai 60, ciki har da na ƙasashen Larabawa — amma ban da Isra’ila.

Taron zai bai wa mahalarta damar "tattauna" iya ci-gaban da aka samu kan sauyi a gwamnatin Falasɗinawa, in ji jami’in.

Ƙungiyar Tarayyar Turai ita ce ta babbar mai tamaka wa gwamnatin Falasɗinawa,kuma ta gindaya sharaɗin cewa duk wani tallafi na gaba kawo gyara wanda take ganin yana da muhimmanci ga gwamnatin falasɗinawa ta taka tata rawar wajen samar da mafita ta ƙasashe biyu ga rikicin Isra’ila da Falasɗinu wanda Turai ta daɗe tana goyon baya.

 

Rumbun Labarai
Ministan Tsaron Ƙasa na Isra'ila na so a hana kiran sallah a masallatan ƙasar
Iran ta ce ta kama wani jirgin ruwa ɗauke da lita miliyan 4 ta fetur da aka yi fasa-ƙwauri a Gulf
Waiwaye kan 2025: Shekarar kisan ƙare dangi a Gaza da sauran yaƙe-yaƙe a duniya
Yara na mutuwa saboda tsananin sanyi a Gaza
Netanyahu ya shiga Masallacin Ƙudus a bikin Ranar  Hanukkah ta Yahudawa 'don tsokana'
Ruwan sama mai tsanani ya kashe aƙalla mutum 10 a Gaza a cikin kwana ɗaya: WHO
Hamas za ta ci gaba da adana makamanta don kariya daga hare-haren Isra'ila a gaba - Jami'in ƙungiyar
Matar Shugaban Ƙasar Turkiyya ta karrama 'yanjarida Falasɗinawa
Babu zaman lafiya idan Falasɗinawa ba su samu 'yanci ba, in ji Shugaban Afirka ta Kudu Ramaphosa
Jirgin Amurka ya mayar da 'yan Iran 55 zuwa Tehran
Jirgi maras matuƙi na Isra'ila ya kashe Falasɗinawa duk da an cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta
Dakarun Isra'ila sun ƙwace kayayyakin tarihi biyar a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye
Cikin Hotuna: An yi bikin auren gomman Falasɗinawa a Gaza a lokaci guda
Rundunar sojin Isra'ila na fuskantar mafi munin matsalar ƙarancin ma'aikata a tarihinta - Janar Brik
Hamas ta ce an kashe masu leƙen asirin Isra’ila huɗu a arewacin Gaza
Sojojin Isra'ila sun yi kisa cikin ruwan sanyi a Jenin, Falasɗinawa sun ambace shi laifin yaƙi
Masu shiga tsakani a yarjejeniyar Gaza suna tattauna mataki na gaba a Masar
Isra’ila ta yi shelar matakin karɓe iko da wani waje mai tarihi a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan
Saudiyya ta ce sai an samar da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta kafin ta ƙulla alaƙa da Isra'ila
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Rubio na matsa wa UAE lamba domin tsagaita wuta a Sudan