| hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Saudiyya ta ce sai an samar da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta kafin ta ƙulla alaƙa da Isra'ila
Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman ya bayyana cewa yiwuwar Saudiyya ta shiga yarjejeniyar Abraham Accords ya danganta ne ga “shirin samar da ƙasashe biyu.”
Saudiyya ta ce sai an samar da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta kafin ta ƙulla alaƙa da Isra'ila
Yarima Mohammed ya ce ƙsarsa tana aiki domin daidaita dangantaka da isra’ila "alokaci mafi kusa da hakan zai yiwu".
19 Nuwamba 2025

Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman ya ce masarautarsa na son ta dawo da alaƙa da Isra’ila ta wata yarjejeniya mai suna Abrahams Accords da Shugaban Amurka Donald Trump ke jagoranta, amma da farko tana buƙatar “bayyananniyar hanya” ga samun ƙasar Falasɗinu.

"Muna son mu kasance cikin yarjejeniyar Abraham Accords. Amma muna son mu samu tabbacin cewa mun samu hanyar samar da zaman lafiya ta hanyar kafa ƙasashe biyu," kamar yadda yarima mai jiran gadon na Saudiyya, ya bayana a fadar White House inda ya gana da Trump ranar Talata.

"Za mu yi aiki a kan wannan, domin tabbatar da cewa za mu shirya yanayi mai kyau nan ba da jimawa ba," in ji shi.

Yayin da Trump wanda ya ce baƙonsa "na da fata mai kyau ga Abraham accords,” ya sake matsawa, sai yariman ya ce: "Muna son zaman lafiya ga Isra’ilawa. Muna son zaman lafiya ga Falasɗinawa."

"Muna son su zauna lafiya a yankin, kuma za mu yi iya ƙoƙariunmu domin kai wa ga wannan ranar."

Saudiyya dai tana maimaita cewa samar da ƙasar Falasɗinawa ce manufarta.

Netanyahu kuma ya daɗe da adawa da batun samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kansu, duk da amince wa ta je-ka-na-yi-ka da y yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da Trump tya tsara wacce ke tangal-tangal.

Netanyahu na jagorantar gwamnatin wata gamayyar jam’iyyun da ke da magoya baya masu tsattsauran ra’ayi, waɗanda suka yi watsi da kafa ƙasar Falasɗinu, amma suna son Isra’ila ta karɓe iko da Gaɓar Yamma da Kogin jordan.

Jonathan Panikoff, tsohon mataimakin shugaban ɓangaren bayanan sirri na cibiyar nazari kan Gabas Ta Tsakiya mai suna Middle East, ya ce Trump zai yi kira ga bin Salman ya matsa kusa da daidata dangantaka da Isra’ila, kuma duk wani rashin ci-gaba a wannan fannin ba zai hana ƙulla sabuwar yarjejeniyar tsaro tsakanin Amurka da Saudiyya ba.

"Buƙatar Shugaba Trump ta sanya jari a Amurka, wadda yarima mai jiran gadon ya yi alƙawarin zubawa a baya, za ta iya samar da yanayi na faɗaɗa dangantaka ta tsaro yayin da shugaban zai yi ƙoƙarin dawo da dangataka tsakanin Saudiyya da Isra’ila," in ji Panikoff,  wanda yanzu yake cibiyar nazari ta Atlantic Council a Washington.

 

Rumbun Labarai
Isra'ila ta kashe fararen-hula 114 a Lebanon bayan saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta: MDD
Mayakan Houthi sun ba da alamar dakatar da kai har kan Isra'ila da jiragen ruwa a Tekun Maliya
Israila ta rushe gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da sabon hari a Khan Younis
Trump ya ce “nan ba da jimawa ba” za a samar da dakarun tsaro na ƙasa da ƙasa a Gaza
Sau 27 Yahudawa 'yan-kama-wuri-zauna suka kutsa Masallacin Kudus a watan da ya wuce - Falasdinu
Bayanai na hukuma sun nuna cewa sojojin Isra'ila sun yi yunkurin kashe kansu sau 279 cikin wata 18
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta