| hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Turkiyya na jimamin tunawa da rasuwar Ataturk shekara 87 da suka wuce
Shugaban Turkiyya da shugabannin siyasa da manyan jami’an shari’a da jami’an soji da sauran wakilan ƙasa sun taru a Anitkabir a birnin Ankara domin karrama Mustafa Kemal Ataturk, da ya assasa ƙasar kuma shugabanta na farko.
Turkiyya na jimamin tunawa da rasuwar Ataturk shekara 87 da suka wuce
Erdogan ya ajiye fure mai launin ja da fari da aka sarrafa kamar tutar Turkiyya a kabarin Ataturk.
10 Nuwamba 2025

Mustafa Kemal Ataturk, wanda ya assasa jamhuriyyar Turkiyya, ana jimamin tunawa da shi ranar Litinin bayan ya shekara 87 da rasuwa inda aka yi wani biki na ƙasa a hukumance a Anitkabir, inda kabarinsa yake a babban birnin ƙasar Ankara.

An fara bikin ne wanda Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, ya halarta tare da shugaban majalisar dokoki Numan Kurtulmus, da ‘yan majalisar ministoci da shugabannin jam’iyyar siyasa da manyan jami’an fannin shari’a da kwamandodin soji.

Erdogan ya ajiye fure mai launin fari da ja da aka sarrafa kamar tutar Turkiyya kan kabarin Ataturk.

Da misalin ƙarfe 9.05 na safiya (ƙarfe 06:05 agogon GMT), lokacin da Ataturk ya rasu, waɗanda suka halarci taunawar sun yi shiru na wani lokaci, kuma bayan haka suka rera waƙar ƙasar. A lokacin yabo, an yi ƙasa-ƙasa da tutar Turkiyya.

Daga bisani, Erdogan da jami’an da suka raka shi sun nufi Benen Misak-i Milli, inda ya saka hannu a Littafin Tunawa na Anitkabir, inda ya yaba wa Ataturk da abokan gwagwarmayarsa.

"Muna tsananin kare Jamhuriyar Turkiyya, wanda ka kira ‘aikinka mai girma,’ kuma mun ci gaba da ƙawata ko wane inci na ƙasarmu da sabbin nasarori," kamar yadda Erdogan ya rubuta.

"A ƙarƙashin shugabancin ƙwararrun mutane, Turkiyya tana ci gaba da taku na aminci a kan hanyarta ta zama ƙasa mai ƙarfi a duniya," a cewarsa.

Ataturk ya kasance shugaban ƙasar na farko har zuwa ranar 10 ga watan Nuwamba na shekarar 1938, lokacin da ya rasu yana mai shekara 57 sakamakon wata cuta ta hanta da ake ce wa cirrhosis a Ingilishi.

Mutanen Turkiyya suna da al’adar zuwa kabarinsa a duk ranar 10 ga watan Nuwamba domin girmama wanda ya assasa ƙasar.

 

 

Rumbun Labarai
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro
Turkiyya ta yi maraba da amincewar majalisar dokokin TRCN kan ƙudurin samar da ƙasashe biyu
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan