| hausa
KASUWANCI
2 minti karatu
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Ma’aikatar Ƙwadago ta ce za a dawo da ma’aikatan da aka kora bakin aiki a dukkan sassan kamfanin Dangote ba tare da tauye wani kudi da za a biya su ba.
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Ma'aikatan a gaban matatar mai ta Dangote da ke binin Legas na Nijeriya.
1 Oktoba 2025

Kungiyar Ma’aikatan Mai a Nijeriya ta amince ta janye yajin aikin da ta tsunduma bayan wata ganawa da ta yi da mahukuntan kamfanin man Dangote da jami’an gwamnati, kamar yadda Ma’aikatar Ƙwadago ta kasar ta bayyana.

An tsunduma yajin aikin ne bayan da Matatar Mai ta Dangote - wadda ita ce mafi girma a nahiyar Afirka mai karfin tace danyen mai ganga 650,000 a kowace rana - ta kori ma'aikatan kungiyar fiye da 800.

Rikicin ya yi barazana ga samar da man fetur da kasuwanci a fadin yammacin Afirka.

Ma’aikatar Ƙwadagon ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar bayan wani zaman sulhu tsakanin kungiyar ta PENGASSAN da kamfanin mai na Dangote, inda ta ce za a dawo da ma’aikatan da aka kora aiki a wasu sassan rukunin Dangote ba tare da asarar albashinsu ba.

Ministan Ƙwadagon ya shaida wa taron cewa kafa kungiya hakki ne na ma’aikata don haka ya kamata a mutunta matakin.

Sanarwar ta kara da cewa "PENGASSAN ta amince ta fara shirin janye yajin aikin."

An kori ma’aikatan matatar mai na Dangote a ranar Alhamis saboda kafa kungiya, inji PENGASSAN a ranar Juma’a.

A lokacin korar jami’an matatar man Dangote sun bayyana cewa korar ma’aikatan wani bangare ne na sake fasalin ma’aikatan tare da zargin wadanda abin ya shafa da yin zagon kasa.

Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji