| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
Qatar tare da Amurka da Tarayyar Afirka sun shafe watanni suna gudanar da jerin tattaunawa don kawo ƙarshen rikici a gabashin DRC mai arzikin ma'adinai, inda M23 ta ƙwace manyan birane.
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
Qatar ta karɓi baƙuncin tattaunawa daban-daban tsakanin gwamnatin DRC da M23 tun watan Afrilu.
15 Nuwamba 2025

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da 'yan tawayen M23 sun rattaɓa hannu kan wata yarjejeniyar da nufin samar da zaman lafiya da kuma kawo ƙarshen yaƙi.

An sanya hannu kan yarjejeniyar a ranar Asabar wadda wakilai daga ɓangarorin biyu suka saka hannu wa a wani taro a babban birnin Qatar, Doha.

Qatar tare da Amurka da Tarayyar Afirka sun shafe watanni suna gudanar da jerin tattaunawa don kawo ƙarshen rikici a gabashin DRC mai arzikin ma'adinai, inda M23 ta ƙwace manyan birane.

‘Yan tawayen na M23 a wani mataki da suka ɗauka na baya-bayan nan da goyon bayan maƙwabciyar Kongo wato Rwanda, sun ƙwace birnin Goma a watan Janairu, birni mafi girma a gabashin DRC, inda suka ci gaba da ƙwace wasu garuruwa a lardunan Kivu ta Arewa da Kivu ta Kudu.

Tun bayan sake ɗaukar makami a ƙarshen 2021, rukunin M23 ya ƙwace manyan yankuna a gabashin DRC tare da tallafin Rwanda, abin da ya haddasa mummunan rikicin jinƙai.

Rwanda ta musanta cewa tana tallafa wa M23

A yayin bikin ƙulla yarjejeniyar a Doha, babban mai sulhu na Qatar, Mohammed Al-Khulaifi, ya kira yarjejeniyar "ta tarihi", yana mai cewa masu shiga tsakani za su ci gaba da ƙoƙari don tabbatar da zaman lafiya a fagen.

Dubban mutane sun mutu a wani farmaki da M23 ta kai a watan Janairu da Fabrairu, wanda a ciki kungiyar ta kwace manyan biranen lardi na Goma da Bukavu.

Yarjejeniyar watan Yuli da aka sanya wa hannu a Doha ta biyo bayan wata ta daban, yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin gwamnatocin DRC da Rwanda da aka rattaɓa wa a Washington a watan Yuni.

Qatar ta karɓi baƙuncin tattaunawa daban-daban tsakanin gwamnatin DRC da M23 tun watan Afrilu.

A watan Oktoba, sun cim ma yarjejeniya kan yadda za a sa ido a kan tsagaita wuta

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi