| hausa
KASUWANCI
2 minti karatu
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Tallafin, daga Asusun Raya ƙasashen Afirka, zai ba da gudunmawar kashi na farko na shirin Gudanar da Harkokin Makamashi da shirin tallafa wa tattalin arzikin ƙasa.
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta Makamashi da Tattalin Arziki
2 Oktoba 2025

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta samu kusan CFA biliyan 81 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 145 daga Bankin Raya Ƙasashen Afirka (AfDB) domin inganta fannin makamashinta da kuma tallafa wa ci gaban tattalin arziki.

Firaiministan kasar Ali Mahamane Lamine Zeine da shugaban AfDB Sidi Ould Tah ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar a Abidjan a ranar Laraba.

Tallafin, daga Asusun Raya Afirka, zai ba da gudunmawar kashi na farko na shirin Gudanar da Harkokin Makamashi da shirin tallafa wa tattalin arzikin ƙasa.

Shirin na da nufin fadada hanyoyin samar da wutar lantarki, da inganta harkokin tattalin arziki, da karfafa rawar da kamfanoni masu zaman kansu ke takawa wajen ci gaban Nijar.

A halin yanzu kashi 22.5% na ‘yan Nijar ne ke samun wutar lantarki, kuma Shirin ya ƙuduri aniyya mayar da hankali wajen samar kashi 30% nan da shekarar 2026, tare da samar da megawatt 50 na makamashin hasken rana a shekarar, sai kuma megawatt 240 nan da shekarar 2030.

Firaiminista Ali Mahamane Lamine Zeine ya ce sauye-sauyen za su haifar da ci gaba mai ɗorewa tare da inganta yanayin rayuwa, yayin da shugaban bankin AfDB, Sidi Ould Tah ya jaddada ci gaba da goyon bayan bankin na dogon lokaci.

Baya ga makamashi, yarjejeniyar ta hada da matakan bunƙasa kudaɗen haraji, da biyan basussukan cikin gida, da kuma bunƙasa ci-gaban kamfanoni masu zaman kansu.

Wannan yunƙurin dai wani babban mataki ne a ƙoƙarin da gwamnatin Nijar ke yi na samar da ci gaba mai ma'ana da kuma 'yanci na makamashi.

Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji