| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Rundunar hadakar soji da Saudi ke jagoranta ta kai hari kan 'yan-awaren da UAE ke goyon baya a Yemen
Rundunar hadakar soji da Saudiyya ke jagoranta ta kai hari kan 'yan-awaren STC da UAE ke goyon baya a Yemen
Rundunar hadakar soji da Saudi ke jagoranta ta kai hari kan 'yan-awaren da UAE ke goyon baya a Yemen
Rundunar hadakar soji da Saudi ke jagoranta ta kai hari kan 'yan-awaren da UAE ke goyon baya a Yemen / AP
2 Janairu 2026

Rundunar hadakar soji da Saudiyya ke jagoranta ta kai wasu munanan hare-hare kan 'yan awaren Majalisar Wucin Gadi ta Kudancin kasar (STC) da kasar Hadaddiyar Daular Larabawa ke mara wa baya a Yemen, inda suka kashe akalla mutum bakwai.

Mohammed Abdulmalik, shugaban rundunar STC a Wadi Hadramaut da Hamadar Hadramaut, ya ce hare-haren sama guda bakwai sun afka wa sansanin Al-Khasah, inda suka kashe mutum bakwai tare da raunata fiye da 20.

Ya ƙara da cewa ƙarin hare-hare sun fada kan wasu wurare a wannan yanki.

Mace-macen su ne na farko da aka samu ƙarƙashin rundunar haɗin gwiwa ta soji da Saudiyya ke jagoranta tun lokacin da STC ta kwace yankunan lardunan Hadramaut da Mahra a watan da ya gabata

Gwamnan Hadramaut Salem al-Khanbashi ya ce an kai hare-haren saman ne da nufin samun dakarun da suka kai hari kan sassan “Dera Al-Watan” yayin da suke kutsawa don ƙwace iko da sansanonin soji.

Ya kuma yi kira ga mazauna Hadramaut da su guji tsoma baki ga rundunonin ko kwanton ɓauna yayin da ake tura su bakin aiki.

Khanbashi ya sanar da kai harin ne jim kadan bayan naɗa shi ya jagoranci rundunar 'National Shield' da Saudiyya ke tallafawa a wannan lardi mai arzikin albarkatun ƙasa da ke kan iyakar Saudiyya.

STC ta ce tun da fari an saka dakarunta cikin shirin ko-ta-kwana bayan da gamayyar soji da Saudiyya ke jagoranta, wadda aka amince da ita a duniya, ta sanar da kai harin don ƙato sansanonin soji a lardin.

Tura jiragen ruwa a Tekun Larabawa

A halin yanzu, Rundunar Sojin Ruwa ta Masarautar Saudiyya ta tura jirage a Tekun Larabawa don fara ayyukan bincike da yaki da fataucin kayayyaki, in ji mai magana da yawun kawancen soji na Larabawa karkashin jagorancin Saudiyya.

Turki al-Maliki a shafin X ya ce tura jiragen ruwa yana nufin karfafa sa ido a teku da aiwatar da ayyukan samame domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a yankin.

Haka kuma a ranar Jumma'a, jakadan Saudiyya a Yemen, Mohammed Al Jabir ya ce STC ta hana wata tawaga daga Riyadh sauka a filin jirgin Aden, inda ya zargi kungiyar da 'rashin sassauci'.

Saudiyya 'ta sha fuskantar ƙin amincewa da rashin sassauci daga shugaban (SCT) Aidaros Alzubidi, a kwanan nan kan ƙin bayar da izinin jirgi da ke ɗaukar tawagar jami'an Saudiyya', Al Jabir ya wallafa a X.

Rumbun Labarai
Iran ta ce ta kama wani jirgin ruwa ɗauke da lita miliyan 4 ta fetur da aka yi fasa-ƙwauri a Gulf
Waiwaye kan 2025: Shekarar kisan ƙare dangi a Gaza da sauran yaƙe-yaƙe a duniya
Yara na mutuwa saboda tsananin sanyi a Gaza
Netanyahu ya shiga Masallacin Ƙudus a bikin Ranar  Hanukkah ta Yahudawa 'don tsokana'
Ruwan sama mai tsanani ya kashe aƙalla mutum 10 a Gaza a cikin kwana ɗaya: WHO
Hamas za ta ci gaba da adana makamanta don kariya daga hare-haren Isra'ila a gaba - Jami'in ƙungiyar
Matar Shugaban Ƙasar Turkiyya ta karrama 'yanjarida Falasɗinawa
Babu zaman lafiya idan Falasɗinawa ba su samu 'yanci ba, in ji Shugaban Afirka ta Kudu Ramaphosa
Jirgin Amurka ya mayar da 'yan Iran 55 zuwa Tehran
Jirgi maras matuƙi na Isra'ila ya kashe Falasɗinawa duk da an cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta
Dakarun Isra'ila sun ƙwace kayayyakin tarihi biyar a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye
Cikin Hotuna: An yi bikin auren gomman Falasɗinawa a Gaza a lokaci guda
Rundunar sojin Isra'ila na fuskantar mafi munin matsalar ƙarancin ma'aikata a tarihinta - Janar Brik
Hamas ta ce an kashe masu leƙen asirin Isra’ila huɗu a arewacin Gaza
Sojojin Isra'ila sun yi kisa cikin ruwan sanyi a Jenin, Falasɗinawa sun ambace shi laifin yaƙi
Masu shiga tsakani a yarjejeniyar Gaza suna tattauna mataki na gaba a Masar
Isra’ila ta yi shelar matakin karɓe iko da wani waje mai tarihi a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan
Turai na shirin horas da ‘yan sandan Falasɗinawa 3,000   bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Saudiyya ta ce sai an samar da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta kafin ta ƙulla alaƙa da Isra'ila
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Rubio na matsa wa UAE lamba domin tsagaita wuta a Sudan