| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Kuɗin da aka biya daga wani asusun tallafin cirani da gudun hijira zai kasance karo na farko na tura kuɗi tsakanin gwamnati zuwa gwamnati daga asusun, in ji sanatan.
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Shugabn ƙasar Equatorial Guinea Teodoro Obiang Nguema Mbasogo
11 Nuwamba 2025

Gwamnatin Shugaba Trump ta tura dala miliyan 7.5 ga gwamnatin ƙasar Equatorial Guinea yayin da take neman ta tasa ƙeyar mutane zuwa ƙasar ta Yammacin Afirka da kuma matsawa kusa da shugabanninta da Amurka ta ƙaƙaba wa takunkumi, in ji wata babbar sanata a kwamitin harkokin wajen na majalisar dattawan ƙasar.

Sanata Jeanne Shaheen, ta bayyana a wata wasiƙar da ta tura ranar Litinin ga Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio cewa “wannan tura kuɗin wanda ya saɓa wa al’ada sosai ya janyo wata babbar damuwa game da amfani da dalolin Amurkawa masu biyan haraji."

Shaheen ta bayyana a wasiƙarta cewa biyan dala miliyan 7.5 ya fita daban domin zai “zarce sosai adadin tallafin da Amurka ta bayar cikin shekaru takwas da suka wuce” ga ƙasar.

Kuɗin, wanda aka biya daga asusun tallafi na cirani da gudun hijira, zai kasance karo na farko da aka tura kuɗi daga gwamnati zuwa gwamnati daga asusun, wanda majalisar dokokin ta assasa a matsayin martani ga matsalar jinƙai.

Ta yi tambaya kan ko biyan kuɗi hanya ce da ta dace a kashe kuɗin Amurka a kai.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ƙi tsokaci game da cikakken bayani kan tattaunawa ta diflomasiyyar, amma ta ce, “ƙaddamar da manufofin shige da fice da gwamnatin Amurka abu ne da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fi bai wa fifiko.

“Kamar yadda Sakatare Rubio ya faɗa, babu ja da baya a jajircewarmu na kawo ƙarshen shiga Amurka ba bisa ƙa’ida ba da kuma shigowar mutane da yawa tare da ƙarfafa tsaron kan iyakokin Amurka.”

Gwamnatin Trump, yayin da take ƙoƙarin ƙara yawan mutanen da take kora daga ƙasar ta nemi ƙulla yarjejeniyoyi da wasu ƙasashe domin su kar karɓi ‘yan ciranin da ba ‘yan ƙasarsu ba ne.

Ƙungiyoyin ‘yan gwagwarmaya sun soki manufa “ta ƙasa daban” a matsayin wata dabara mara tunani.

Nijeriya dai ta ƙi amincewa da yarjejeniyar inda kwanakin baya Ministan Hrkokin Wajen ƙasar Yusuf Tuggar ya ce Nijeriya ta ƙi ne saboda matsalolinta sun ishe ta ba sai ta karɓi masu laifuka ‘yan wasu ƙasashe daga Amurka ba.

Baya ga tasa ƙeyar mutanen, Amurka na ƙoƙarin rage tasirin China a Equatorial Guinea da kuma bunƙasa harkar man Amurka a ƙasar.

 

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD