KASUWANCI
2 minti karatu
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
Turkiyya ce ƙasa ta shida a Turai wajen yawan tashi da saukar jiragen sama, inda jirage kiman 3,992 suke tashi a kowacce rana a tsakanin 23 da 29 ga Yuli, in ji Abdulkadir Uraloglu.
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
Filin tashi da saukar jiragen sama na Istanbul
4 Yuli 2025

Filin jiragen saman Istanbul ne mafi samun hada-hada a Turai a mako gudan da ya gabata, inda ake da tashi da saukar jirage 1,553, in ji Ministan Sufuri da Zuba Jari na ƙasar Abdulkadir Uraloglu a ranar Juma’a.

Filin jiragen sama na Istanbul ya wuce na Charles de Gaulle da ke Paris, da Frankfurt a Jamus da Heathrow na Landan a tsakanin 23 da 29 ga Yuni.

A jerin sunayen da aka fitar, filin jiragen saman Antalya ne na 10 da yake da tashin jiragen sama 996 a kowace rana.

Uraloglu ya ce rahoton da aka fitar daga Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Jiragen Sama ta Turai da ya kunshi bayanan 23 zuwa 29 ga Yuni, a jimlace Turkiyya ce ƙasa ta shida a jerin ƙasashen Turai a bangaren tashi da saukar jiragen sama, inda take da zirga-zirgar jirage 3,992 a kowace rana, inda ta yi zarra kan ƙasashe irin su Girka, da Netherland, da Poland.

Mahadar yanki da duniya

“A yanzu Turkiyya ba wai ƙasar bi ta cikin ta ba ne kawai a sufurin jiragen sama, ta zama mahaɗar yanki da duniya baki ɗaya.” in ji shi.

Ya bayyana cewa matsakaicin adadin tashi da saukar jiragen sama ya ƙaru da kashi 15 idan aka kwatanta da gabanin annobar Covid-19.

Ya kuma ce Turkiyya na daya daga cikin kasashen da suka koma matakin da suke tun kafin ɓarkewar annobar Korona.

Uraloglu ya kuma bayyana cewa filin jiragen saman Istanbul ne na bakwai a duniya a tsakanin manyan filayen jiragen sama 25, inda take da tashin jiragen sama 773 a tsakanin 23 da 29 ga Yuni.

 

Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji