AFIRKA
2 minti karatu
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
Dakarun Garde Nationale na Nijar ne suka gudanar da waɗannan ayyuka a yankin Agadez bayan samun sahihan bayanan sirri game da wata mota da ke tafe daga Libya wadda ake zargi tana ɗauke da muggan makamai.
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
Waɗannan nasarori na nuna himmar dakarun Nijar wajen tabbatar da tsaron ƙasar daga barazanar kan iyaka.
14 awanni baya

Rundunar tsaro ta Garde Nationale ta Nijar ta samu nasara har sau biyu a yankin Agadez na ƙasar. Dakarun rundunar sun gudanar da manyan ayyuka guda biyu: na farko, cafke wata mota daga Libya ɗauke da makamai da harsasai masu yawa, sannan kuma sai kama wasu masu safarar miyagun ƙwayoyi dauke da sunƙin tabar wiwi mai yawa.

Waɗannan nasarori na nuna himmar dakarun Nijar wajen tabbatar da tsaron ƙasar daga barazanar kan iyaka.

A ranar 5 ga Nuwamba, bayan samun sahihan bayanan sirri game da wata mota da ke tafe daga Libya wadda ake zargi, an tura dakaru na musamman na Garde Nationale domin sa ido da aikin kame kilomita 65 arewa maso gabashin Agadez.

Bayan sun bi motar da ake zargi na tsawon lokaci, an tsayar da ita. A cikin motar, an cafke wasu masu safarar makamai uku ɗauke da muggan makamai masu yawa.

Makaman sun haɗa da bindigar Machine Gun da AK-47 biyu da fiye da harsasar 9,400 iri daban-daban da wayoyi tara  da katan uku na sigari da kuɗaɗen ƙasashen waje iri daban-daban da aka ɓoye a cikin kayayyakin masu safarar.

A cewar hukumomin yankin, wannan kamen ya nuna rawar da Agadez ke takawa a hanyoyin kasuwancin Sahara da kuma yadda dakarun Nijar suka ƙara kaimi wajen yaki da safarar abubuwa ta kan iyaka.

A mako guda kafin wannan, a ranar 27 ga Oktoba, 2025, wani aiki da dakarun na Garde Nationale suka yi ya kai ga kama masu safarar miyagun ƙwayoyi guda biyu dauke da ƙwallayen tabar wiwi 63 da kuma babura guda biyu da suke amfani da su wajen wannan haramtacciyar sana’a.

Waɗannan kamen da aka yi a jere suna tabbatar da yadda ayyukan Garde Nationale ke ƙaruwa a yankin, inda laifukan da ake aikatawa na kan iyaka – ciki har da safarar makamai, miyagun ƙwayoyi da mutane – suka zama babban ƙalubale ga tsaro.

Rundunar, wadda ke kan gaba wajen yaƙi da laifuka a yankunan hamada, ta tabbatar ta hanyar waɗannan ayyuka cewa tana da ƙudurin dakile duk wata barazana ga tsaron ƙasa.

Rumbun Labarai
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar
Nijar da Chadi za su ƙaddamar da aikin yi wa dabbobi rigakafi a Diffa