| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Shugaba Tinubu ya tafi Faransa da Ingila don fara hutun shekara-shekara na kwana 10
A watan Oktoban shekarar 2024 ma shugaban na Nijeriya ya tafi hutun shekara-shekara na mako biyu.
Shugaba Tinubu ya tafi Faransa da Ingila don fara hutun shekara-shekara na kwana 10
A shekarar 2023 ne Shugaban Bola Tinubu ya karɓi ragamar mulkin Nijeriya. / Nigeria Presidency
4 Satumba 2025

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya fara hutun shekara-shekara ranar Alhamis 4 ga watan Satumba na wannan shekarar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Nijeriya, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafinsa na X, ta ce shugaban zai shafe kwanakin aiki goma yana hutun na shekara-shekara.

 “Shugaba Tinubu zai yi hutun ne tsakanin Faransa da Birtaniya kana ya dawo ƙasar [Nijeriya],” in ji sanarwar.

Daga bisani shugaban na Nijeriya ya tashi daga Abuja inda ya nufi Turai a jirgin shugaban ƙasa.

Tun da ya hau karagar mulki, shugaban Nijeriya ya yi tafiya-tafiye sosai.

A watan Oktoban shekarar 2024 ma shugaban na Nijeriya ya tafi hutun shekara-shekara na mako biyu.

 A wancan lokacin, wata sanarwa da Onanuga ya fitar ta ce shugaban zai tafi Birtaniya ne domin yin hutun.

“Zai yi amfani da makonnin biyun ne a matsayin hutun aiki da kuma lokacin tunani game da garambawul ɗin tattalin arziin gwamnatinsa,” in ji sanarwar da Onanuga ya fitar a wancan lokacin.