| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 15% kan shigar da fetur da dizal cikin ƙasar
Tun farko manufar wannan matakin ita ce ƙarfafa masana’antun tace man cikin gida kamar su Matatar Dangote da ƙananan masana’antun tace mai, ta hanyar sanya man da ake shigar da shi daga waje ya fi tsada.
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 15% kan shigar da fetur da dizal cikin ƙasar
NMDPRA ta gargaɗi masu son ɓoye man fetur ɗin da masu rige-rigen sayen fetur ɗin domin farbagar ƙarewa kan cewa akwai wadataccen man a ƙasar.
4 awanni baya

Hukumar kula da harkokin sarrafawa, tacewa da sufurin man fetur ta Nijeriya, NMDPRA a ranar Alhamis ta bayyana cewa ta jingine aniyarta ta aiwatar da harajin kashi 15 cikin ɗari da aka tsara a kan shigar da man fetur daga waje zuwa cikin ƙasar.

Daraktan Sashen Harkokin Jama’a na NMDPRA, George Ene-Ita ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar, inda ya yi gargadin jama’a da su guji sayen man da gaggawa saboda tsoron ƙarewa.

A ranar 29 ga Oktoba, Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da saka harajin shigo da man fetur da dizal — wata manufa da ake sa ran za ta ƙara farashin shigo da man daga ƙasashen waje.

Tun farko manufar wannan matakin ita ce ƙarfafa masana’antun tace man cikin gida kamar su Matatar Dangote da ƙananan masana’antun tace mai, ta hanyar sanya man da ake shigar da shi daga waje ya fi tsada. An tsara fara aiwatar da wannan manufa ne a ranar 21 ga Nuwamban 2025.

Sai dai a wani sabon bayani, NMDPRA ta ce gwamnati ta daina la’akari da ci gaba da aiwatar da harajin shigo da man fetur.

“Ya kamata a lura cewa aiwatar da harajin kashi 15 cikin ɗari a kan shigo da Man Fetur da Diesel ba ya cikin shirin gwamnati a yanzu,” in ji wani ɓangare na sanarwar.

A cikin sanarwar, hukumar ta NMDPRA ta tabbatar wa jama’a cewa akwai wadataccen man fetur a ƙasar a matakin da aka amince a daidai wannan lokacin da ake matuƙar buƙatar fetur ɗin.

Haka kuma hukumar ta gargaɗi masu son ɓoye man fetur ɗin da masu rige-rigen sayen fetur ɗin domin farbagar ƙarewa kan cewa akwai wadataccen man a ƙasar.

 

Rumbun Labarai
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka