| hausa
Ra'ayi
AFIRKA
5 minti karatu
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
Tsarin da duniya ke tafiya a kai yau ba ya samar da mafita ko yin adalci. An ga haka a Gaza, kafin sannan an gani a Bosnia da Rwanda. A yanzu ana sake shaida hakan a Sudan.
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
Alkaluma a hukumance sun ce an kashe sama da mutane 2,000 a Al fasher.
11 Nuwamba 2025

Abin da ke faruwa a yau a Al Fasher, a kowace fuska, laifi ne ns cin zarafin bil'adama. Akwai shaidu masu karfi da ke nuna cewa RSF ta aikata manyan laifuka na take hakkin bil'adama kuma ta aikata ayyuka kai tsaye da suka saba wa dokokin yaƙi.

A cikin mako guda kacal, an kashe dubban mutane a gaban idanun duniya. Wannan, a kowace fuska, bala'i ne ga bil'adama.

Duk da haka, wannan ba shi ne karo na farko da Sudan ta shaida irin wannan bala’i ba. Tsawon watanni goma sha takwas da suka gabata, mutanen Al Fasher ke ƙarƙashin mamaya, suna mutuwa a hankali. Ba sa iya samun abinci.

A wani lokaci, an tilasta musu cin abincin dabbobi har ma da naman birai, beraye, da maguna. A wani kaulin, tun kafin kisan kiyashin na yau, an riga an fara wani salon kisan cikin jinkiri. A wannan matakin, yana da muhimmanci a fahimci irin tunani da yanayin tunanin da ke haifar da ta’addancin 'yan tawayen RSF.

Rugujewar adalci a duniya da matsayar Turkiyya

Turkiyya, tare da ƙasashe da dama da ke ƙaruwa, ta fara yin magana don nuna goyon baya ga al'ummar Sudan game da ta'asar da RSF ke yi.

Wannan yana nuna tsarin da Turkiyya ke bi wajen mayar da hankali kan manufofin ƙasashen waje.

A duk lokacin wani rikici a duniya, daga Sudan zuwa Gaza, muryar Turkiyya ta kasance mai ƙarfafa gwiwa da kuma bayyana halayya ta kwarai.

Dole ne a yarda cewa Shugaba Recep Tayyip Erdoğan yana cikin shugabannin duniya kaɗan da suka ci gaba da bayyana wa duniya irin mummunan halin jinkai da ake ciki a Sudan.

Abin takaici, wasu kaɗan ne suka yi irin haka. Majalisar Dinkin Duniya, a halin yanzu, ta sake gaza yin aiki yadda ya kamata.

Abin baƙin ciki, duniya ta saba da irin wannan gurguwar fahimta. Tambayar gaskiya ba ita ce ko ƙasashen duniya za su iya shiga tsakani ba, a’a shin suna son yin hakan.

Tsarin da duniya ke tafiya a kai yau ba ya samar da mafita ko yin adalci. An ga haka a Gaza, kafin sannan an gani a Bosnia da Rwanda. A yanzu ana sake shaida hakan a Sudan.

Rashin ɗaukar matakan ladabtarwa kan laifukan yaƙi da Firamiinistan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya aikata a Gaza na iya zama mafi bayyananniyar alamar wannan lalacewa. Amincewar jama'a ga tsarin shari'a na duniya ta rushe.

Babu wani matakin dakatar da waɗanda suke aikata ta'asa. Kowace rugujewar al’umma ta fara ne da lalacewar halayya, kuma tsarin duniya a yau yana tafiya a kan hakan.

Muhimmancin El-Fasher da darussan da aka yi watsi da su

El-Fasher yna da matuƙar muhimmanci. Idan kuka kalli taswira za kua shaida yana ya nuna garin a matsayin babbar hanyar shiga cibiyar hhada-hada da safarar kayayyaku., musamman a yanzun sa uke yaki ‘ya’addar RSF.

Duk da haka, yana da mahimmanci a lura cewa manyan yankunan Darfur masu arzikin zinare suna cikin Jebel Amir da Songo.

Muhimmancin Al Fasher ba ya dogara ne akan albarkatunta ba, amma yana matsayin mahaɗar gabas da yamma na Sudan.

Haka kuma yana da filin jirgin sama wanda ke da mahimmanci wajen gudanar da ayyuka.

Darfur ya ƙunshi manyan birane biyar. Al Fasher ne babban birnin Arewacin Darfur. Har zuwa makon da ya gabata, shi ne kawai birnin Darfur da ke ƙarƙashin ikon sojoji yayin da RSF sun riga sun mamaye Kudu, Yamma, Tsakiya, da Gabashin Darfur.

Bayan kawanya da aka yi ta tsawon shekara ɗaya da rabi, RSF ta karɓe iko da Al Fasher, ta mayar da dukkan Darfur ƙarƙashin ikonta. Saboda haka, faɗuwar birnin ba wai kawai alama ce ba; wani sauyi ne na siyasa.

A lokaci guda, abin da ake gani a Al Fasher ba komai ba ne illa karar da wata kabila. Akwai ƙa'idodin yaƙi amma mayakan RSF sun yi watsi da su. Shiga tsakani nan take na ƙasashen duniya yana da mahimmanci.

Hotunan tauraron ɗan adam sun nuna kaburbura da kisan gilla da yawa. Hana samun ƙarin ta'addanci da kare haƙƙin ɗan adam sun zama dole ne yanzu kuma ya kamata su zama babban fifikon kasashen duniya.

Zuwa yanzu, dukkan alamu sun nuna cewa RSF za ta ci gaba da karya dokokin jinkai na duniya da kuma ƙa'idodin rayuwar ɗan adam.

Misali, rahotanni sun nuna cewa wani shugaban 'yan bindiga da ake kira da "Abu Lulu" ya kashe tare da bayar da umarnin kashe fararen hula marasa adadi. Wannan lamari ne guda ɗaya kawai a tsakanin mutane da yawa. Babban batun shi ne rashin takunkumi mai tasiri.

Bayan ayyukan Isra'ila a Gaza, rashin aikin "dokokin kasa da kasa" ya bayyana fiye da kowane lokaci.

Ƙungiyoyi kamar RSF suna samun ƙarfin gwiwa daga wannan rashin bin doka domin ba sa yin aiki su kaɗai. Rahotanni da yawa, ciki har da waɗanda Majalisar Dinkin Duniya ta bayar, sun bayyana goyon bayan da suke samu daga kasashen waje.

A yau, ana shaida wata Gaza, amma a wannan karon a Sudan, a Al Fasher. Inda ake da irin dauin gindin da Isra'ila ke da shi, dokar ƙasa ta ruguje. A wannan lokacin, tsammanin bin dokokin yaƙi ko girmama haƙƙin ɗan adam ya zama mafarki.

Abin da ke faruwa a Al Fasher a yau shi ne ɗan adam yana shigar da kansa kara gaba shari’a. Kuma a cikin wannan shari'ar, wanda ake tuhuma ba wai kawai RSF ba ne, har ma da tsarin duniya da ya yi shiru yana kallo ba tare da yin komai ba.

Marubucin, Tunç Demirtaş malami ne a sashen Hulɗar Ƙasashen Duniya a Jami'ar Mersin, Turkiyya.

Togaciya: Ba lallai ra’ayin da marubucin ya bayyana ya zama ya yi daidai da ra’ayin dab’i na TRT Afrika ba. 

Rumbun Labarai
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD