| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Kamfanin dillancin labaran ƙasar Ghana ya ambato ministan yana cewa “adadin kuɗin da gwamnatin za ta kashe a shekarar zai kasance cedi biliyan 302.5."
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Ministan kuɗin Ghana, Dakta Cassiel Ato Forson , ne ya gabatar da kasafin kuɗi a majalisar dokokin ƙasar a madadin Shugaban ƙasar
14 Nuwamba 2025

Ministan Kuɗin Ghana Dakta Cassiel Ato Forson ya gabatar da kasafin kuɗin gwamnatin ƙasar na shekarar 2026 ga majalisar dokoki a madadin Shugaba John Dramani Mahama.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar Ghana ya ambato ministan yana cewa “adadin kuɗin da [gwamnatin] za ta kashe zai kasance GHc biliyan 302.5.”

Kuɗin zai kai kimanin naira tiriliyan 40 idan aka sauya shi zuwa naira daga kuɗin Ghana.

Dakta Forson ya ce kasafin kudin ya nuna wani babban sauyi  daga “farfaɗowa zuwa canji, da kuma juriya zuwa himmar aiki da kuma ɗorewar ayyukan yi,” yana mai bayyana matakan ƙarfafa ɗorewar tattalin arziki da hanzarta samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa fannonin zamantakewa.

“An yi ƙiyasin cewa albashin ma’aikata zai kai GHc biliyan 90.3 (kimanin naira triliyan 12), domin tabbatar da biya da ya dace ga ma’ikatan gwamnati,” in ji ministan kuɗin.

Ya bayyana cewa gwamnatin ta sake dawo da tsarin tsimi a fannin kuɗi da daidaita kuɗin cedi da rage hauhawar farashi da kuma sake ƙara ƙarfafa ƙwarin gwiwar masu zuba jari.

Kazalika ya ce kuɗaɗen da gwamnatin Ghana ke son kashewa kan ababen more rayuwa GHc biliyan 57.5 (kimanin naira tiriliyan 7.4 idan aka sauya kuɗin zauwa naira).

Ministan ya ce kasafin kuɗin shekarar 2026 ya mayar da hankali ne kan abubuwa uku masu muhimmanci — tsimi mai ɗorewa a harkar kuɗi da kula da bashi yadda ya dace da kuma zuba jari a kan ababen more rayuwa da harkar noma domin samar da ayyukan yi da kuma inganta ilimi da lafiya da tsaro da ci-gaba na bai ɗaya.

A shekarar 2026 dai gwamnatin ƙasar tana sa ran samun kuɗi da ya kai GHc biliyan 286.1( kimanin naira tiriliyan 37) ta hanyar haraji.

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi