KASUWANCI
3 minti karatu
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji
Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokoki huɗu masu muhimmanci da ke da manufar kwaskwarima ga tsarin tattara haraji a ƙasar a ranar Alhamis.
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji
Shugaba Tinubu yayin sanya hannu kan sababbin Dokokin Harajin a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja
26 Yuni 2025

A yayin wani taro da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Abuja babban birnin Nijeriya a ranar Alhamis, shugaban Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokokin haraji da aka yi wa kwaskwarima, waɗanda a baya suka janyo ce-ce-ku-ce a faɗin ƙasar.

An ɗauki tsawon lokaci gwamnatin ƙasar mai jihohi 36 na son kwaskwarima ga tsarin tattara haraji a kasar, tana mai cewa sabon tsarin zai daidaita karba da rarraba haraji a fadin kasar.

"Tsawon lokaci, tsarin harajinmu ya kasance wani abu mara tsari mai kyau - mai rikitarwa, wanda babu adalci, da dora nauyi," Tinubu ya bayyana haka a wani sako da ya fitar ta shafukan sada zumunta kafin sanya hannun.

Tinubu ya yi alkawarin samun sauki ga talakawa da masu aiki a Najeriya.

Sauye-sauyen da shugaban kasar ya yi tun da farko sun hada da janye tallafin man fetur mai tsada da kuma sassauta farashin canjin Naira -- ya samu yabo daga masana tattalin arziki da ke cewa an ma makara wajen daukar irin wadannan matakai.

Amma kuma matakan sun haifar da hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa a Nijeriya.

Dokokin hudu su ne – Dokar Harajin Najeriya, da Dokar Kula da Ayyukan Harajin Najeriya, da Dokar Kafa Hukumar Tattara Haraji ta Kasa, da Dokar Hukumar Kula da Haraji ta Kasa ta Hadin gwiwa.

Dokokin za su kara yawan kudaden da ake samu a kasar, sanna za kuma su rage nauyin biyan haraji kan masu karamin karfi, in ji wani kwararre kan harkokin haraji Chukuemeka Eze a yayin tattunawa da AFP.

Yayin da kasar ke fuskantar matsalolin tattalin arziki mafi muni cikin shekarun da suka gabata, sabbin dokokin sun kebe kananan ‘yan kasuwa masu karamin karfi daga biyan harajin kamfanoni da kuma rage harajin kamfanoni zuwa kashi 25 cikin dari daga kashi 30 cikin dari.

Gwamnatin ta kuma kawo tsarin bai daya na tattara haraji tare da sauya fasalin rabon kudaden shiga tsakanin gwamnatin tarayya da gwamnatocin Jihohi.

An yi watsi da manyan sauye-sauyen tsarin rabon kudaden shiga yayin da kudurorin suka je hannun majalisun dokoki na kasa, bayan da aka fahimci yadda kudu da arewacin aksar suka bambanta da juna ta fuskar arziki, addini da kabila.

Daya daga cikin dokokin sun sauya sunan Hukumar Tattara ta Cikin Gida ta Nijeriya zuwa Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (NRS), inda mahukunta suka ce manufar hakan ita ce karfafa yanayin samun kudaden shiga, duk da cewa kudaden da gwamnatin tarayya ke samu daga harajin (VAT) zai ragu, inda za a ware karin kudade ga daidaikun jihohi.

Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci