KASUWANCI
2 minti karatu
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Farashin ya ragu zuwa Naira 800,000 ($521) kan kowane ton a ranar Alhamis, wanda ya yi ƙasa da kashi 33 cikin ɗari daga farashin da aka sayar kwanaki kaɗan da suka gabata.
Farashin ƙwallon kaɗanya ya faɗi warwas a Nijeriya bayan ƙasar ta dakatar da fitar da shi
Burkina Faso, Ghana, Mali, Ivory Coast da Togo na daga cikin ƙasashen da suka taƙaita fitar da ƙwallonm kaɗanya
30 Agusta 2025

Farashin ƙwallon kaɗanya, wanda ake amfani da shi a kayan kwalliya da kuma kayan zaƙi, ya fadi a Nijeriya bayan gwamnatin ƙasar ta shiga sahun sauran ƙasashen Yammacin Afirka wajen hana fitar da shi ƙasashen waje.

A cewar Rildwan Bello, Shugaban kamfanin Vestance da ke Legas, wanda ke bibiyar farashin kayayyakin gona ya ce farashin ya ragu zuwa Naira 800,000 ($521) kan kowane ton a ranar Alhamis, wanda ya yi ƙasa da kashi 33 cikin ɗari daga farashin da aka sayar kwanaki kaɗan da suka gabata.

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa an sanya haramcin watanni shida ne domin “tabbatar da isasshen kaya ga masu sarrafa shi a cikin gida da samar da ayyukan yi, da kuma kare harkar da mata ne suka fi rinjaye wajen tattara shi da kashi 95 cikin 100.”

Sai dai Bello ya ce, duk da cewa manufar gwamnatin ƙasar mai kyau ce, hakan zai haifar da matsalolin kuɗi ga manyan ‘yan kasuwa da ke fitar da shi, waɗanda yanzu za su iya samun matsala musamman ga waɗanda suka samu kwangilar fitar da shi.
“Fitar da shi waje ce ke sa kasuwar ta yi armashi. Abin da ake buƙata a cikin gida bai kai kai adadin wanda ake samu ba,” in ji shi.

“Kirkirar masana’antu ba abu bane da ake yi a cikin dare ɗaya. Ba za ka iya kafa masana’antar sarrafawa cikin wata biyu kawai ba.

Itatuwan da ke bada ƙwallon kaɗanya suna girma a hankali kuma asalinsu daga Afirka ta Yamma ne. Nijeriya na samar da ton 500,000 a duk shekara, in ji bayanan gwamnati. Sauran manyan masu samarwa sun hada da Burkina Faso, Ghana, Mali, Ivory Coast da Togo, waɗanda duka suka taƙaita fitar da shi domin ƙarfafa sarrafa cikin gida.

Tun bayan hawan Tinubu a watan Mayun 2023, shugaban na ta ƙoƙarin fara samar da ayyukan yi ta hanyar taƙaita sayar da albarkatu zuwa ƙasashen waje. Ya ce, wannan haramcin zai taimaka wajen daidaita matsalar da Nijeriya ke da ita inda take samar da kusan kashi 40 na kwallon kaɗanya, amma tana da kashi kasa da 1% na kasuwar duniya mai darajar dala biliyan 6.5.

Rumbun Labarai
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa
Gwamnatin ƙasar Ghana ta ƙara farashin koko
Nijar ta samu tallafin $145m daga bankin AfDB domin inganta makamashi da tattalin arziki
Elon Musk na dab da zama mutum na farko da arzikinsa ya kai tiriliyan a duniya: rahoto
Dangote zai mai da ma'aikatan Matatar Mai da aka kora daga aiki - Ma'aikatar Ƙwadagon Nijeriya
Kamfanin Orano na Faransa ya ce ya tara tan 1,500 na uranium a Nijar
Kamfanonin haɗin gwiwa ƙarƙashin Saudiyya za su sayi kamfanin wasannin game na Electronic Arts (EA)
Kamfanin Turkish Airlines zai sayi jiragen sama na Boeing 225 bayan Trump da Erdogan sun tattauna
Hukumomi a Ghana sun kama mutanen da ake zargi da yin fasa-ƙwaurin zinari
Matatar mai ta Dangote ta yi watsi da jita-jitar dakatar da aiki na wasu watanni
Babban Bankin Ghana ya dakatar da lasisin cinikin kuɗin ƙetare na UBA da wasu manhajojin aika kuɗi
Babban Bankin Ghana ya ba da sabbin sharuɗɗan kuɗaɗen ƙetare ga masu shiga da kayayyaki
Madogarar bincike kan abincin da aka sauya wa halitta (GMO), da dalilan karɓuwarsa a Nijeriya
Manoman koko a Ghana sun fi takwarorinsu samun farashi mai kyawu a Yammacin Afirka – COCOBOD
Nijeriya na sa ran ganin sakamako mai kyau bayan aiwatar da wani kyakkyawan tsari a harkar kamfanoni
Kamfanin Tsaro na Turkiyya zai ƙulla yarjejeniya da Malaysia don samar mata da motocin yaƙi
Turkiyya da Libya sun kulla yarjejeniyar hakar ma’adanai, samar da makamashi da ababen more rayuwa
Filin jiragen sama na Istanbul ya sake cirar tutar tashin jirage a Turai, in ji Ministan Sufuri
China da Amurka sun cim ma yarjejeniyar kasuwanci
Shugaban Nijeriya Tinubu ya sanya hannu a kan sababbin Dokokin Haraji