| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun ciro gawarwaki 27 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe
Dakarun rundunar Bataliya ta 241, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro da na ceto na gida sun yi gaggauwar isa wurin kana suka yi saurin kai ɗauki, a cewar wata majiya.
Sojojin Nijeriya sun ciro gawarwaki 27 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe
Kwale-kwale / Reuters
5 Janairu 2026

Dakarun sojojin Nijeriya sun ceto mutum 13 da ransu kana sun ciro gawarwaki 27 bayan hatsarin wani jirgin kwale-kwale a ƙaramar hukumar Nguru ta jihar Yobe da ke yakin Arewa maso gabashin Nijeriya.

Wata majiya mai tushe a rundunar sojin kasar ce ta bayyana haka ga Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Litinin a Abuja.

Majiyar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:15 na safe a ranar Lahadi 4 ga Janairun 2026, lokacin da kwale-kwalen dauke da akalla 'yankasuwa 40 daga kauyen Adiani da ke Jigawa zuwa wata kasuwa a Nguru ya kife a yankin kogin Garbi.

Dakarun rundunar Bataliya ta 241, tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro da masu nutso na gida sun yi gaggauta isa wurin kana suka yi saurin kai ɗauki, in ji majiyar.

"Aikin haɗin gwiwar binciken da aka gudanar da kuma kokarin ceto mutanen ya kai ga nasarar ceto mutum 13 da rai, yayin da aka ciro gawarwaki 27 daga kogin."

Tuni dai aka binne wadanda suka rasa rayukansu bisa tsari na addinin Musulunci, yayin da hukumomin da abin ya shafa ke daukar karin matakan da suka dace.

Rumbun Labarai
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump