| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
Lamarin ya faru a daren Asabar lokacin da wani kwale-kwale ɗauke da fasinjoji 52 ya kife yayin da yake tafiya tsakanin jihar Jigawa zuwa Jihar Yobe.
Aƙalla mutane 25 sun mutu, an ceto 13 a hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe ta Nijeriya
At least 25 have been killed in a boat accident in Nigeria on January 3, 2026. / Reuters
4 Janairu 2026

Akalla mutane 25 ne aka tabbatar sun mutu a wani hatsarin kwale-kwale a Jihar Yobe na Najeriya, in ji jami'ai a ranar Lahadi.

Lamarin ya faru a daren Asabar lokacin da wani kwale-kwale ɗauke da fasinjoji 52 ya kife ya kuma nutse yayin da yake tafiya daga garin Adiyani a Karamar Hukumar Guri ta jihar Jigawa zuwa Garbi a Karamar Hukumar Nguru ta jihar Yobe.

An ceto fasinjoji 13, yayin da rahoton farko na jami'ai ya ce ana ci gaba da neman mutane 14 har yanzu.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe, Mohammed Goje ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu cewa mutanen sun tafi kamun kifi ne, da noma, da sauran harkokin kasuwanci, lokacin da kwale-kwalen ya kife da su a tsakiyar ruwa.

“ Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe na iya tabbatar da wannan mummunan hatsarin kwale-kwale da ya faru a cikin kogi a Nguru,” in ji Goje.

“Tawagarmu ta bincike da ceton har yanzu na aiki tare da hukumomin tsaro da 'yan sa-kai na al'umma don nemo waɗanda suka ɓace,” in ji Goje.

Rumbun Labarai
Fiye da mutum 50 ne suka mutu a harin 'yan bindiga a jihar Neja ta tsakiyar Nijeriya
‘Yansandan Nijeriya sun gayyaci Fasto Chris Okafor bisa zarge-zargen aikata fyaɗe
Nijeriya ta kama Indiyawa 22 bisa zargin shigar da hodar ibilis ƙasar
An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: 'yansanda
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri
Sakon Shugaba Tinubu na Sabuwar Shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya
Abin da bincike ya gano na musabbabin annobar cutar ƙoda a Jihar Yobe
Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar
Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey da ke Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Usmaniyya ta Turkiyya
Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje
Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba  Jam'iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Bam da aka binne a titi ya halaka mutane a Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Mun tuntuɓi Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu 'yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma'aikatar Harkokin Waje
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donald Trump